< 2 Sama’ila 4 >

1 Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
Or, Isboseth, fils de Saül, apprit qu’Abner avait succombé à Hébron, et ses mains perdirent leur force, et tout Israël fut troublé.
2 To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
Cependant il y avait deux hommes, chefs de voleurs, auprès du fils de Saül; le nom de l’un était Baana, et le nom de l’autre, Réchab, fils de Remmon, le Bérothite, des fils de Benjamin, puisque Béroth aussi était réputée de Benjamin.
3 domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
Et les Bérothites s’enfuirent à Géthaïm, et ils ont été là comme étrangers jusqu’à ce temps-ci.
4 (Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
Or, Jonathas, fils de Saül, avait un fils, infirme des pieds; il avait cinq ans, quand vint de Jezraël la nouvelle touchant Saül et Jonathas; c’est pourquoi sa nourrice, le prenant, s’enfuit; et, comme elle se hâtait de fuir, il tomba, et devint boiteux; et il eut pour nom Miphiboseth.
5 To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
Etant donc venus, les fils de Remmon, le Bérothite, Réchab et Baana, entrèrent, à la chaleur du jour, dans la maison d’Isboseth, qui dormait sur son lit à midi; et la portière de la maison, vannant du blé, s’endormit.
6 Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
Ils entrèrent donc dans la maison secrètement, prenant des épis de froment; et Réchab et son frère le frappèrent à l’aîne, et s’enfuirent,
7 Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
Ainsi lorsqu’ils furent entrés dans la maison, Isboseth dormait sur son lit dans sa chambre à coucher; et, le frappant, ils le tuèrent; puis, sa tête enlevée, ils s’en allèrent par la voie du désert, durant toute la nuit,
8 Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
Et ils apportèrent la tête d’Isboseth à David à Hébron, et ils dirent au roi: Voici la tête d’Isboseth, fils de Saül, votre ennemi, qui cherchait votre âme: et le Seigneur a vengé aujourd’hui mon seigneur le roi de Saül et de sa race.
9 Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
Mais David répondant à Réchab et à Baana son frère, fils de Remmon, le Bérothite, il leur dit: Le Seigneur vit, lui qui a délivré mon âme de toute angoisse!
10 sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
Celui qui m’avait annoncé et dit: Saül est mort, et qui pensait qu’il annonçait une heureuse nouvelle, je le pris et le tuai à Siceleg, lui à qui il fallait donner une récompense pour son message;
11 Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
Combien plus maintenant que des hommes impies ont tué l’homme innocent, dans sa maison, sur son lit, demanderai-je son sang à votre main, et vous enlèverai-je de la terre!
12 Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.
C’est pourquoi David ordonna à ses serviteurs, et ils les tuèrent; et coupant leurs mains et leurs pieds, ils les suspendirent! à la piscine, à Hébron; mais la tête d’Isboseth, ils la prirent et l’ensevelirent dans le sépulcre d’Abner à Hébron.

< 2 Sama’ila 4 >