< 2 Sama’ila 4 >

1 Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
Quand le fils de Saül eut appris qu'Abner était mort à Hébron, ses mains devinrent lâches, et tout Israël fut étonné.
2 To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
Or le fils de Saül avait deux capitaines de bandes, dont l'un avait nom Bahana, et l'autre Récab, fils de Rimmon Béerothien, des enfants de Benjamin; car [la ville de] Béeroth était aussi réputée de Benjamin.
3 domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
Et les Béerothiens s'étaient enfuis à Guittajim, et ils y ont fait leur séjour jusqu'à aujourd'hui.
4 (Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
Et Jonathan, fils de Saül avait un fils blessé aux pieds, âgé de cinq ans, lorsque le bruit [de la mort de] Saül et de Jonathan vint de Jizréhel; et sa gouvernante le prit, et s'enfuit; et comme elle se hâtait de fuir, il tomba, et devint boiteux; et il fut nommé Méphiboseth.
5 To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
Récab donc et Bahana fils de Rimmon Béerothien vinrent, et entrèrent pendant la chaleur du jour dans la maison d'Is-boseth, qui prenait son repos du midi.
6 Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
Ainsi Récab et Bahana son frère entrèrent jusqu'au milieu de la maison, allant prendre du froment, et ils le frappèrent à la cinquième côte, et se sauvèrent.
7 Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
Ils entrèrent donc dans la maison, lorsque Is-boseth était couché sur son lit, dans la chambre où il dormait, et ils le frappèrent, et le tuèrent; puis ils lui ôtèrent la tête, et la prirent, et ils marchèrent par le chemin de la campagne toute cette nuit-là.
8 Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
Et ils apportèrent la tête d'Is-boseth à David à Hébron, et ils dirent au Roi: Voici la tête d'Is-boseth fils de Saül ton ennemi, qui cherchait ta vie; et l'Eternel a aujourd'hui vengé le Roi mon Seigneur, de Saül et de sa race.
9 Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
Mais David répondit à Récab et à Bahana son frère, enfants de Rimmon Béerothien, et leur dit: L'Eternel qui a délivré mon âme de toute angoisse, est vivant;
10 sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
Que je saisis celui qui vint m'annoncer et me dire: Voilà, Saül est mort, et qui pensait m'apprendre de bonnes nouvelles et je le tuai à Tsiklag, ce qui fut le salaire que je lui devais donner pour ses bonnes nouvelles.
11 Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
Combien plus [dois-je faire punir] ces méchants qui ont tué un homme de bien dans sa maison, sur son lit? Maintenant donc ne redemanderai-je pas son sang de votre main, et ne vous exterminerai-je pas de la terre?
12 Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.
David donc fit commandement à ses gens, lesquels les tuèrent et leur coupèrent les mains et les pieds, et les pendirent sur l'étang d'Hébron. Puis on prit la tête d'Is-boseth, et on l'ensevelit au sépulcre d'Abner à Hébron.

< 2 Sama’ila 4 >