< 2 Sama’ila 4 >
1 Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
Quand le fils de Saül eut appris qu’Abner était mort à Hébron, les bras lui tombèrent; tout Israël aussi fut consterné.
2 To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
Parmi les chefs de bande du fils de Saül se trouvaient deux hommes ayant nom l’un Baana, l’autre Rêkhab, deux Benjamites, fils de Rimmon le Beérotite; car Beérot aussi était attribué à Benjamin.
3 domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
Les Beérotites s’étaient réfugiés à Ghittayim, où ils ont résidé jusqu’à ce jour.
4 (Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
(Jonathan, fils de Saül, avait laissé un fils boiteux; ce dernier avait cinq ans lorsqu’arriva, de Jezreël, la nouvelle relative à Saül et à Jonathan; sa nourrice l’emporta en fuyant, le laissa tomber dans sa précipitation, et il devint boiteux; il se nommait Mephiboseth.)
5 To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
Or, les fils de Rimmon le Beérotite, Rêkhab et Baana, s’acheminèrent vers la demeure d’Isboseth, où ils arrivèrent au plus chaud de la journée; il était couché, goûtant le repos de midi.
6 Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
Rêkhab et son frère Baana pénétrèrent jusque dans l’intérieur de la maison en acheteurs de froment, le frappèrent dans l’aine et se sauvèrent.
7 Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
Ils y étaient entrés comme il reposait sur son lit, dans sa chambre à coucher, l’avaient frappé à mort et lui avaient coupé la tête. Munis de cette tête, ils s’en allèrent par la plaine et marchèrent toute la nuit.
8 Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
Ils apportèrent à David, à Hébron, la tête d’lsboseth, et dirent au roi: "Voici la tête d’Isboseth, fils de Saül, ton ennemi, qui en voulait à ta vie. Dieu a vengé en ce jour mon seigneur le roi de Saül et de sa postérité."
9 Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
David répondit à Rêkhab et à Baana, son frère, fils de Rimmon le Beérotite, en ces termes: "Par le Dieu vivant, qui a sauvé ma personne de tous les dangers!
10 sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
celui qui m’annonça que Saül était mort, se croyant porteur d’une bonne nouvelle, je le fis saisir et tuer à Ciklag, le payant ainsi de sa bonne nouvelle;
11 Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
combien plus, quand des méchants ont fait périr un homme de bien dans sa maison, sur sa couche! Et maintenant, certes, je vous demanderai compte de son sang et vous ferai disparaître du pays."
12 Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.
Sur l’ordre de David, les serviteurs les mirent à mort, leur coupèrent les mains et les pieds et les pendirent près de l’étang de Hébron; quant à la tête d’Isboseth, ils la prirent pour la déposer dans le sépulcre d’Abner, à Hébron.