< 2 Sama’ila 4 >

1 Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
Then Ishbosheth, the son of Saul, heard that Abner had fallen in Hebron. And his hands were weakened, and all of Israel was troubled.
2 To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
Now the son of Saul had two men, leaders among robbers. The name of the one was Baanah, and the name of the other was Rechab, sons of Rimmon, a Beerothite from the sons of Benjamin. For indeed, Beeroth, too, was reputed with Benjamin.
3 domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
And the Beerothites had fled into Gittaim. And they were strangers there, until that time.
4 (Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
Now Jonathan, the son of Saul, had a son with disabled feet. For he was five years old when the report about Saul and Jonathan arrived from Jezreel. And so, his nurse, taking him up, fled. And while she was hurrying, so that she might flee, he fell and was made lame. And he was called Mephibosheth.
5 To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
And so, the sons of Rimmon the Beerothite, Rechab and Baanah, arrived and entered the house of Ishbosheth, in the heat of the day. And he was sleeping on his bed at midday. And the doorkeeper of the house, who was cleaning the wheat, fell fast asleep.
6 Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
Then they entered the house secretly, taking the ears of grain. And Rechab and his brother Baanah stabbed him in the groin, and they fled away.
7 Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
For when they had entered the house, he was sleeping on his bed in a closed room. And striking him, they killed him. And taking his head, they departed by the way of the desert, walking throughout the night.
8 Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
And they brought the head of Ishbosheth to David in Hebron. And they said to the king: “Behold, the head of Ishbosheth, the son of Saul, your enemy, who was seeking your life. And so, the Lord has avenged my lord the king, this day, from Saul and from his offspring.”
9 Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
But David, responding to Rechab and his brother Baanah, the sons of Rimmon the Beerothite, said to them: “As the Lord lives who has rescued my soul from all distress,
10 sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
the one who reported to me and said, ‘Saul is dead,’ who was thinking that he announced good news, I apprehended. And at Ziklag I killed him who ought to have been given a reward for the news.
11 Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
How much more so now, when impious men have put to death an innocent man in his own house, upon his bed, shall I not require his blood from your hand, and take you away from the earth?”
12 Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.
And so, David commanded his servants, and they put them to death. And cutting off their hands and feet, they suspended them up over the pool in Hebron. But the head of Ishbosheth they took and buried in the sepulcher of Abner at Hebron.

< 2 Sama’ila 4 >