< 2 Sama’ila 4 >

1 Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
A když uslyšel Izbozet syn Saulův, že umřel Abner v Hebronu, zemdlely ruce jeho, a všecken lid Izrael byl předěšen.
2 To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
Měl pak syn Saulův dva muže hejtmany nad dráby, jméno jednoho Baana, a jméno druhého Rechab, synové Remmona Berotského z synů Beniamin; nebo i Berot počítá se v Beniaminovi.
3 domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
Utekli pak byli Berotští do Gittaim, a byli tam pohostinu až do toho dne.
4 (Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
Měl také byl Jonata syn Saulův syna chromého na nohy, (nebo když byl v pěti letech a přišla pověst o Saulovi a Jonatovi z Jezreel, vzavši ho chůva jeho, utíkala, a když pospíchala utíkajici, on upadl a okulhavěl), jehož jméno Mifibozet.
5 To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
A odšedše synové Remmona Berotského, Rechab a Baana, vešli o poledni do domu Izbozetova. On pak spal na lůžku poledním.
6 Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
A aj, když vešli až do domu, jako by bráti měli obilé, ranili ho v páté žebro, Rechab a Baana bratr jeho, a utekli.
7 Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
Nebo když byli vešli do domu, a on spal na lůžku svém v pokojíku svém, kdež léhal, probodli jej a zabili, a sťavše hlavu jeho, vzali ji, a šli cestou po pustinách celou tu noc.
8 Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
I přinesli hlavu Izbozetovu k Davidovi do Hebronu a řekli králi: Aj, hlava Izbozeta syna Saulova, nepřítele tvého, kterýž hledal bezživotí tvého. Hle, pomstil dnes Hospodin pána mého krále nad Saulem i semenem jeho.
9 Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
Tedy odpovídaje David Rechabovi a Baanovi bratru jeho, synům Remmona Berotského, řekl jim: Živť jest Hospodin, kterýž vysvobodil duši mou ze všech úzkostí,
10 sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
Kdyžť jsem toho, kterýž mi oznámil, řka: Aj, Saul zahynul, (ješto se jemu zdálo, že veselé noviny zvěstuje), vzal a zabil jsem ho v Sicelechu, jemuž se zdálo, že ho budu darovati za poselství:
11 Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
Èím pak více lidi bezbožné, kteříž zamordovali muže spravedlivého v domě jeho na ložci jeho? A nyní, zdaliž nebudu vyhledávati krve jeho z ruky vaší, a nevyhladím vás z země?
12 Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.
I rozkázal David služebníkům, aby je zbili. I zutínali jim ruce i nohy jejich, a pověsili u rybníka při Hebronu. Hlavu pak Izbozetovu vzavše, pochovali v hrobě Abnerově v Hebronu.

< 2 Sama’ila 4 >