< 2 Sama’ila 3 >
1 Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
Torej tam je bila dolga vojna med Savlovo hišo in Davidovo hišo, toda David je postajal močnejši in močnejši, Savlova hiša pa je postajala šibkejša in šibkejša.
2 An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
Davidu so se v Hebrónu rodili sinovi. Njegov prvorojenec je bil Amnón; od Jezreélke Ahinóam;
3 na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
in njegov drugi Kiláb od Abigájile, žene Karmelčana Nabála in tretji Absalom, sin Maáhe, hčere gešurskega kralja Talmája;
4 na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
in četrti Adoníja, Hagítin sin; in peti Šefatjá, sin Abitále;
5 na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
in šesti Jitreám od Davidove žene Egle. Ti so bili rojeni Davidu v Hebrónu.
6 Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
Pripetilo se je, medtem ko je bila vojna med Savlovo hišo in Davidovo hišo, da je Abnêr sebe naredil močnega za Savlovo hišo.
7 To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
Savel je imel priležnico, ki ji je bilo ime Ricpa, Ajájeva hči in Iš Bošet je rekel Abnêrju: »Zakaj si odšel k priležnici mojega očeta?«
8 Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
Potem je bil Abnêr zelo ogorčen zaradi besed Iš Bošeta in je rekel: » Mar sem pasja glava, ko ta dan zoper Juda izkazujem prijaznost hiši tvojega očeta Savla, njegovim bratom in njegovim prijateljem in te nisem izročil v Davidovo roko, da me danes obsojaš s krivdo glede te ženske?
9 Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
Tako stori Bog Abnêrju in še več, razen če, kakor je Gospod prisegel Davidu, celo tako jaz storim njemu,
10 Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
da se kraljestvo prestavi od Savlove hiše in da postavi Davidov prestol čez Izraela in čez Juda, od Dana, celo do Beeršébe.«
11 Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
In ni mogel Abnêrju ponovno odgovoriti besede, ker se ga je bal.
12 Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
Abnêr pa je v svojem imenu poslal poslance k Davidu, rekoč: »Čigava je ta dežela?« Rekoč tudi: »Skleni zavezo z menoj in glej, moja roka bo s teboj, da k tebi privedem ves Izrael.«
13 Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
Rekel je: »Dobro. Jaz bom sklenil zavezo s teboj, toda od tebe zahtevam eno stvar, to je: ›Ne boš videl mojega obraza, razen če mi najprej ne pripelješ Savlove hčere Mihále, ko prideš, da vidiš moj obraz.‹«
14 Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
David je poslal poslance k Savlovemu sinu Iš Bošetu, rekoč: »Izroči mi mojo ženo Mihálo, ki sem si jo zaročil za sto prednjih kožic Filistejcev.«
15 Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
Iš Bošet je poslal in jo vzel od njenega soproga, torej od Lajiševega sina Paltíela.
16 Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
Njen soprog je odšel skupaj z njo, jokajoč za njo, do Bahuríma. Potem mu je Abnêr rekel: »Pojdi, vrni se.« In se je vrnil.
17 Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
Abnêr je imel pogovor z Izraelovimi starešinami, rekoč: »V preteklih časih ste iskali za Davidom, da bi bil kralj nad vami.
18 To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
Sedaj torej to storite, kajti Gospod je govoril o Davidu, rekoč: ›Po roki svojega služabnika Davida bom rešil svoje ljudstvo Izraela iz roke Filistejcev in iz roke vseh njihovih sovražnikov.‹«
19 Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
Abnêr je govoril tudi na ušesa Benjamina in Abnêr je odšel, da govori tudi na Davidova ušesa v Hebrónu. Vse to se je zdelo dobro Izraelu in to se je zdelo dobro celotni Benjaminovi hiši.
20 Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
Tako je Abnêr prišel k Davidu v Hebrón in z njim dvajset mož. David je naredil zabavo za Abnêrja in može, ki so bili z njim.
21 Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
Abnêr je rekel Davidu: »Vstal bom in šel in ves Izrael bom zbral k svojemu gospodu kralju, da bodo lahko s teboj sklenili zavezo in da boš lahko kraljeval nad vsem, kar si tvoje srce želi.« David je poslal Abnêrja proč in ta je odšel v miru.
22 Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
Glej, Davidovi služabniki in Joáb so prišli iz zasledovanja krdela in s seboj prinesli velik plen, toda Abnêr ni bil z Davidom v Hebrónu, kajti poslal ga je proč in ta je odšel v miru.
23 Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
Ko so prišli Joáb in vsa vojska, ki je bila z njim, so Joábu povedali, rekoč: »Nerov sin Abnêr je prišel h kralju in ta ga je poslal proč in je odšel v miru.«
24 Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
Potem je Joáb prišel h kralju in rekel: »Kaj si storil? Glej, Abnêr je prišel k tebi. Zakaj je to, da si ga poslal proč in je on popolnoma izginil?
25 Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
Ti poznaš Nerovega sina Abnêrja, da je prišel, da te zavede in da spozna tvoja odhajanja in tvoja prihajanja in da spozna vse, kar delaš.«
26 Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
Ko je Joáb prišel od Davida, je za Abnêrjem poslal poslance, ki so ga ponovno privedli od vodnjaka Sire. Toda David tega ni vedel.
27 To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
Ko se je Abnêr vrnil v Hebrón, ga je Joáb vzel na stran, v velika vrata, da bi tiho govoril z njim in ga tam udaril pod petim rebrom, da je umrl zaradi krvi njegovega brata Asaéla.
28 Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
Potem ko je David to slišal, je rekel: »Jaz in moje kraljestvo sva brez krivde pred Gospodom na veke pred krvjo Nerovega sina Abnêrja.
29 Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
Ta naj počiva na Joábovi glavi in na vsej hiši njegovega očeta in naj iz Joábove hiše ne zmanjka tistega, ki ima izliv ali je gobavec ali se naslanja na palico ali pada na meč ali mu primanjkuje kruha.«
30 (Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
Tako sta Joáb in njegov brat Abišáj umorila Abnêrja, ker je ubil njunega brata Asaéla v bitki pri Gibeónu.
31 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
David je rekel Joábu in vsemu ljudstvu, ki je bilo z njim: »Pretrgajte svoja oblačila in se opašite z vrečevino in žalujte pred Abnêrjem.« In sam kralj David je sledil mrtvaškemu odru.
32 Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
Abnêrja so pokopali v Hebrónu. Kralj je povzdignil svoj glas in jokal nad Abnêrjevim grobom in vse ljudstvo je jokalo.
33 Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
Kralj je žaloval nad Abnêrjem in rekel: »Je Abnêr umrl, kakor umira bedak?
34 Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
Tvoje roke niso bile zvezane niti tvoja stopala, vklenjena v okove. Kakor mož pada pred zlobneži, tako padaš ti.« In vse ljudstvo je ponovno jokalo nad njim.
35 Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
Ko je vse ljudstvo prišlo, da povzročijo Davidu, da jé hrano, medtem ko je bil še dan, je David prisegel, rekoč: »Tako naj mi Bog stori in še več, če okusim kruh ali karkoli drugega, dokler sonce ne zaide.«
36 Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
Vse ljudstvo je to opazilo in to jim je ugajalo, kakor karkoli je kralj storil, je vsemu ljudstvu ugajalo.
37 Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
Kajti vse ljudstvo in ves Izrael je ta dan razumelo, da to ni bilo od kralja, da umori Nerovega sina Abnêrja.
38 Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
Kralj je rekel svojim služabnikom: »Ali ne veste, da je ta dan tukaj v Izraelu padel princ in velik mož?
39 A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”
Jaz sem ta dan šibek, čeprav maziljen kralj in ti možje, Cerújini sinovi, so pretežki zame. Gospod bo hudodelca nagradil glede na njegovo zlobnost.«