< 2 Sama’ila 3 >
1 Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
Krigen mellem Sauls hus og Davids hus blev langvarig; og David blev sterkere og sterkere, men Sauls hus blev svakere og svakere.
2 An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
David fikk seks sønner i Hebron: Hans førstefødte var Amnon, sønn av Akinoam fra Jisre'el.
3 na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
Den annen var Kilab, sønn av Abiga'il, karmelitten Nabals hustru, og den tredje Absalom, sønn av Ma'aka, som var datter til Talmai, kongen i Gesur,
4 na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
den fjerde Adonja, sønn av Haggit, den femte Sefatja, sønn av Abital,
5 na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
og den sjette Jitream, sønn av Davids hustru Egla. Disse sønner fikk David i Hebron.
6 Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
Mens krigen stod på mellem Sauls hus og Davids hus, støttet Abner Sauls hus.
7 To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
Nu hadde Saul hatt en medhustru ved navn Rispa, datter til Aja. Så sa Isboset til Abner: Hvorfor er du gått inn til min fars medhustru?
8 Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
Abner blev harm over Isbosets ord og sa: Er jeg et hundehode som holder med Juda? Den dag idag gjør jeg vel mot Sauls, din fars hus, mot hans brødre og hans venner; jeg har ikke overgitt dig i Davids hånd, og så går du nu i rette med mig for denne kvinnes skyld!
9 Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
Gud la det gå Abner ille både nu og siden om jeg ikke gjør således mot David som Herren har tilsvoret ham,
10 Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
og tar kongedømmet fra Sauls hus og opreiser Davids trone over Israel og over Juda fra Dan like til Be'erseba.
11 Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
Og han torde ikke svare Abner et ord mere, så redd var han for ham.
12 Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
Og Abner sendte bud i sitt sted til David og lot si: Hvem hører landet til? Og han lot fremdeles si: Gjør en pakt med mig, så skal jeg hjelpe dig og få hele Israel til å gå over til dig.
13 Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
Han svarte: Godt, jeg vil gjøre en pakt med dig; bare én ting krever jeg av dig: Du skal ikke komme for mine øine før du har med dig Mikal, Sauls datter, når du kommer for å trede frem for mig.
14 Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
Og David sendte bud til Isboset, Sauls sønn, og lot si: Gi mig min hustru Mikal, som jeg vant mig til brud med hundre filistrers forhuder!
15 Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
Da sendte Isboset bud og tok henne fra hennes mann Paltiel, sønn av La'is.
16 Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
Og hennes mann fulgte med og gikk gråtende bakefter henne like til Bahurim; men Abner sa til ham: Gå hjem igjen! Da vendte han om.
17 Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
Men Abner talte med Israels eldste og sa: Allerede lenge har I ønsket å få David til konge over eder.
18 To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
Så la ham nu bli det! For Herren har sagt om David: Ved min tjener Davids hånd vil jeg frelse mitt folk Israel fra filistrenes og alle deres fienders hånd.
19 Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
Abner talte også med benjaminittene. Så gikk han avsted for å tale med David i Hebron om alt det som Israel og hele Benjamins hus hadde besluttet.
20 Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
Abner kom til David i Hebron med tyve mann, og David gjorde et gjestebud for Abner og de menn som var med ham.
21 Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
Og Abner sa til David: Jeg vil ta avsted og samle hele Israel til min herre kongen, så de kan gjøre en pakt med dig, og du kan råde over alt det du ønsker. Så lot David Abner fare, og han drog bort i fred.
22 Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
I det samme kom Davids folk og Joab hjem fra et herjetog og hadde meget bytte med sig; Abner var da ikke lenger hos David i Hebron, for han hadde latt ham fare, og han hadde draget bort i fred.
23 Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
Da nu Joab og hele hæren som var med ham, kom hjem, fikk Joab høre at Abner, Ners sønn, var kommet til kongen, og at kongen hadde latt ham fare, og at han hadde draget bort i fred.
24 Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
Da gikk Joab inn til kongen og sa: Hvad har du gjort? Abner kom til dig; hvorfor lot du ham da fare sin vei?
25 Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
Du kjenner da Abner, Ners sønn, og vet at han er kommet for å narre dig og for å få rede på all din ferd og alt det du gjør.
26 Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
Så gikk Joab bort igjen fra David og sendte nogen folk avsted som skulde hente Abner, og de førte ham tilbake fra Sira-brønnen; men David visste ikke noget om det.
27 To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
Da nu Abner kom tilbake til Hebron, tok Joab ham til side midt inn i porten for å tale med ham i ro; og der stakk han ham i underlivet, så han døde; det var for å hevne sin bror Asaels blod.
28 Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
Da David siden fikk høre dette, sa han: Jeg og mitt kongedømme er for evig uten skyld for Herren i Abners, Ners sønns blod.
29 Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
La det komme over Joabs hode og over hele hans fars hus, og la det i Joabs hus aldri fattes nogen som har flod eller er spedalsk, eller nogen som går med krykke, eller som faller for sverdet, eller som mangler brød.
30 (Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
Således myrdet Joab og hans bror Abisai Abner, fordi han hadde drept deres bror Asael ved Gibeon under striden.
31 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
Men David sa til Joab og alt folket som var hos ham: Sønderriv eders klær og bind sekk om eder og gå klagende foran Abner! Og kong David gikk selv efter båren.
32 Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
Så begravde de Abner i Hebron, og kongen gråt høit ved Abners grav, og alt folket gråt.
33 Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
Og kongen kvad denne klagesang over Abner: Skulde da Abner dø som en niding dør?
34 Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
Dine hender var ikke bundet og dine føtter ikke lagt i lenker; som en faller for ugjerningsmenn, så falt du. - Og alt folket blev ved å gråte over ham.
35 Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
Så kom alt folket for å få David til å ta mat til sig mens det ennu var dag. Men David svor: Gud la det gå mig ille både nu og siden om jeg smaker brød eller noget annet før solen går ned!
36 Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
Og alt folket forstod det, og de syntes godt om det; alt det kongen gjorde, syntes folket godt om.
37 Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
Og på den dag skjønte alt folket og hele Israel at det ikke var kongen som var ophavsmann til drapet på Abner, Ners sønn.
38 Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
Og kongen sa til sine menn: Vet I ikke at en høvding og stor mann er falt i Israel på denne dag?
39 A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”
Men jeg er ennu svak og bare salvet til konge, og disse menn, Serujas sønner, er mektigere enn jeg. Herren gjengjelde den som gjør ondt, det onde han gjør!