< 2 Sama’ila 24 >
1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
Och Herrans vrede förgrymmade sig åter emot Israel, och gaf David ibland dem in, att han sade: Gack bort, räkna Israel och Juda.
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Och Konungen sade till Joab sin härhöfvitsman: Far omkring i alla Israels slägter, ifrå Dan intill BerSeba, och räkna folket, att jag må veta huru mycket det är.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Joab sade till Konungen: Herren din Gud föröke till detta folket, såsom det nu är, ännu hundrade resor så mycket, att min herre Konungen må se lust deruppå. Men hvad hafver min herre Konungen lust till detta ärendet?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Men Konungens ord måste gå före, emot Joab och höfvitsmännerna öfver hären. Alltså drog Joab ut, och höfvitsmännerna öfver hären ifrå Konungenom, att de skulle tälja Israels folk;
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Och foro öfver Jordan, och lägrade sig i Aroer, på högra sidone vid den staden, som ligger i Guds bäck, och i Jaeser;
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Och kommo till Gilead, och i nederlandet Hadsi; och kommo till DanJaan, och omkring Zidon;
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Och kommo till den fasta staden Tyrus, och till alla de Heveers och Cananeers städer; och kommo ut söder på Juda till BerSeba;
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Och drogo kringom hela landet. Och efter nio månader och tjugu dagar kommo de till Jerusalem igen.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Och Joab fick Konungenom summan af folket, som taldt var; och det var i Israel åttahundrade sinom tusende starke män, som svärd utdrogo; och i Juda femhundrade sinom tusende män.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Och Davids hjerta slog honom, sedan folket taldt var. Och David sade till Herran: Jag hafver svårliga syndat, att jag detta gjort hafver; och nu, Herre, tag bort dins tjenares missgerning; ty jag hafver gjort mycket dårliga.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Och då David stod upp om morgonen, kom Herrans ord till Propheten Gad, Davids Siare, och sade:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Gack bort och tala till David: Så säger Herren: Treggehanda ting sätter jag dig före; utvälj der ett af, det jag dig göra skall.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Gad kom till David, och bådade honom, och sade till honom: Vill du, att hård tid kommer i sju år i ditt land? Eller att du i tre månader måste fly för dina fiendar, och de förfölja dig? Eller att pestilentie blifver i tre dagar i ditt land? Så märk nu, och se till hvad jag skall säga honom igen, som mig sändt hafver.
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
David sade till Gad: Mig är stor ångest; men låt mig falla i Herrans hand; ty hans barmhertighet är stor; jag vill icke falla i menniskohand.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
Alltså lät Herren komma pestilentie i Israel, ifrå morgonen intill bestämdan tid, så att folket blef dödt, ifrå Dan intill BerSeba, sjutiotusend män.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
Och då Ängelen utsträckte sina hand öfver Jerusalem, att han det förderfva skulle, ångrade Herranom det onda, och sade till Ängelen, som folket förderfvade: Det är nog; håll nu din hand tillbaka. Och Herrans Ängel var vid Arauna lado, den Jebuseens.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
Då David såg Ängelen, som folket slog, sade han till Herran: Si, jag hafver syndat; jag hafver gjort den missgerningena; hvad hafva desse fåren gjort? Låt dina hand vara emot mig och mins faders hus.
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Och Gad kom till David i samma tiden, och sade till honom: Gack upp, och res upp Herranom ett altare uti Arauna lado, den Jebuseens.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
Alltså gick David upp, såsom Gad sagt och Herren budit hade.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Och då Arauna vände sig om, såg han Konungen med sina tjenare gå till sig; och tillbad på sitt ansigte ned till jordena;
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Och sade: Hvi kommer min herre Konungen till sin tjenare? David sade: Till att köpa ladona af dig, och bygga Herranom ett altare, att plågan må återvända i folkena.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Arauna sade till David: Min herre Konungen tage och offre såsom honom täckes; si, der äro oxarna till bränneoffer, och slädar, och redskapen till oxarna till ved.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Allt gaf Arauna Konungenom; och Arauna sade till Konungen: Herren din Gud låte dig vara sig behagelig.
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Men Konungen sade till Arauna: Icke så, utan jag vill köpa dig det af för penningar; ty jag vill icke göra Herranom minom Gud bränneoffer, det jag till gifvins hafver. Alltså köpte David ladona, och oxarna, för femtio siklar silfver;
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Och byggde dersammastäds Herranom ett altare; och offrade bränneoffer, och tackoffer. Och Herren vardt landena försonad, och plågan vände åter på Israel.