< 2 Sama’ila 24 >

1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
Men Herrens vrede optendtes atter mot Israel, og han egget David op imot dem og sa: Gå avsted og tell Israel og Juda!
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Da sa kongen til sin hærfører Joab, som var hos ham: Dra omkring i alle Israels stammer fra Dan like til Be'erseba og mønstre folket, så jeg kan få vite tallet på dem!
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Joab svarte: Herren din Gud legge hundre ganger så mange til dette folk som de er nu, så min herre kongen selv får se det! Men hvorfor har min herre kongen fått lyst til dette?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Men kongen holdt fast ved sin befaling og gav ikke efter for Joab og hærførerne. Så drog da Joab og hærførerne ut i kongens tjeneste for å mønstre Israels folk.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
De satte over Jordan og leiret sig ved Aroer, på høire side av den by som ligger midt i Gads-dalen og bortimot Jaser.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Så kom de til Gilead og til lavlandet, som nylig var inntatt; siden kom de til Dan-Ja'an og så rundt om bortimot Sidon.
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Så kom de til Tyrus' festning og til alle hevittenes og kana'anittenes byer; og til sist drog de til sydlandet i Juda, til Be'erseba.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Således drog de om i hele landet og kom efter ni måneder og tyve dager tilbake til Jerusalem.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Og Joab opgav for kongen det tall som var utkommet ved folkemønstringen: I Israel var det åtte hundre tusen sterke menn som kunde dra sverd, og Judas menn var fem hundre tusen.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Men samvittigheten slo David efterat han hadde tellet folket, og David sa til Herren: Jeg har syndet storlig med det jeg har gjort; men tilgi nu, Herre, din tjeners misgjerning; for jeg har båret mig meget uforstandig at.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Da David stod op om morgenen, kom Herrens ord til profeten Gad, Davids seer, og det lød så:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Gå og tal til David: Så sier Herren: Tre ting forelegger jeg dig; velg en av dem, så vil jeg gjøre så mot dig!
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Da kom Gad til David og forkynte ham dette og sa til ham: Vil du at det skal være hungersnød i ditt land i syv år, eller at du skal komme til å flykte for dine fiender i tre måneder, mens de forfølger dig, eller at det skal bli pest i ditt land i tre dager? Tenk nu efter og se til hvad jeg skal svare ham som har sendt mig!
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
David sa til Gad: Jeg er i stor angst; la oss da helst falle i Herrens hånd! For hans barmhjertighet er stor, men i menneskers hånd vil jeg nødig falle.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
Sa lot Herren det komme en pest i Israel, fra morgenen til sammenkomstens tid; og der døde av folket fra Dan til Be'erseba sytti tusen mann.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
Og engelen rakte ut sin hånd mot Jerusalem for å ødelegge det; da angret Herren det onde, og han sa til engelen som gjorde ødeleggelse blandt folket: Det er nok; dra nu din hånd tilbake! Herrens engel var da ved jebusitten Aravnas treskeplass.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
Da David så engelen som slo ihjel blandt folket, sa han til Herren: Det er jeg som har syndet, det er jeg som har gjort ille; men denne min hjord, hvad har de gjort? La din hånd komme over mig og over min fars hus!
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Samme dag kom Gad til David og sa til ham: Gå op og reis Herren et alter på jebusitten Aravnas treskeplass!
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
Så gikk David dit op efter Gads ord, således som Herren hadde befalt.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Da Aravna så ut, fikk han se kongen og hans tjenere som kom over til ham; da gikk Aravna ut og kastet sig ned for kongen med ansiktet mot jorden.
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Og Arvna sa: Hvorfor kommer min herre kongen til sin tjener? David svarte: For å kjøpe treskeplassen av dig og bygge et alter der for Herren, forat hjemsøkelsen kan stanse og vike fra folket.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Da sa Aravna til David: Min herre kongen må ta og ofre hvad han finner for godt! Se, her er oksene til brennofferet og treskesledene og åkene som er på oksene, til ved;
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
alt dette, konge, gir Aravna kongen. Og Aravna sa til kongen: Herren din Gud ta nådig imot dig!
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Men kongen svarte: Nei, jeg vil kjøpe det av dig for penger; jeg vil ikke ofre Herren min Gud brennoffere som jeg har fått for intet. Så kjøpte David treskeplassen og oksene for femti sekel sølv.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Og David bygget der et alter for Herren og ofret brennoffere og takkoffere; og Herren hørte landets bønn, og hjemsøkelsen stanset og vek fra Israel.

< 2 Sama’ila 24 >