< 2 Sama’ila 24 >
1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
Et la fureur du Seigneur recommença à s’irriter contre Israël, et il excita parmi eux, David, disant: Va, dénombre Israël et Juda.
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Le roi dit donc à Joab, prince de son armée: Parcours toutes les tribus d’Israël, depuis Dan jusqu’à Bersabée, et dénombrez tout le peuple, afin que j’en sache le nombre.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Et Joab répondit au roi: Que le Seigneur votre Dieu multiplie votre peuple encore autant qu’il est maintenant, et que de nouveau, il le centuple en la présence de mon seigneur le roi: mais que veut faire mon seigneur le roi par une chose de cette nature?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Mais la parole du roi l’emporta sur les paroles de Joab et des princes de l’armée; et Joab sortit, et les princes des soldats, de la présence du roi, pour dénombrer le peuple d’Israël.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Et lorsqu’ils eurent passé le Jourdain, ils vinrent à Aroër, à la droite de la ville qui est dans la vallée de Gad,
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Puis, par Jazer ils passèrent en Galaad, et dans la terre inférieure d’Hodsi; et ils vinrent dans les forêts de Dan. Tournant ensuite près de Sidon,
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Ils passèrent près des murailles de Tyr, et de toute la terre de l’Hévéen et du Chananéen, et ils vinrent au midi de Juda, à Bersabée.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Et, toute la terre examinée, ils se trouvèrent, après neuf mois et vingt jours, à Jérusalem.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Joab donc donna le dénombrement du peuple au roi, et il se trouva d’Israël huit cent mille hommes forts, qui pouvaient tirer l’épée; et de Juda, cinq cent mille combattants.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Mais le cœur de David fut pris de remords, après que le peuple eut été dénombré, et David dit au Seigneur: J’ai beaucoup péché en cette action; mais je vous prie. Seigneur, écartez l’iniquité de votre serviteur, parce que j’ai agi tout à fait en insensé.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
C’est pourquoi David se leva le matin, et la parole du Seigneur fut adressée à Gad, le prophète et le voyant de David, disant:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Va, et parle à David: Voici ce que dit le Seigneur: L’option de trois choses t’est donnée; choisis celle que tu voudras, afin que je te la fasse.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Lors donc que Gad fut venu vers David, il lui annonça, disant: Ou une famine vous viendra sur la terre durant sept ans; ou vous fuirez vos ennemis durant trois mois, et eux vous poursuivront; ou bien une peste sera pendant trois jours dans votre terre. Maintenant donc délibérez, et voyez quelle parole je dois porter en réponse à celui qui m’a envoyé.
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
Et David répondit à Gad: Je suis dans une très grande angoisse, mais il vaut mieux que je tombe dans les mains du Seigneur (car ses miséricordes sont sans nombre), que dans les mains des hommes.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
Et le Seigneur envoya une peste en Israël, depuis le matin jusqu’au temps marqué; et il mourut d’entre le peuple, depuis Dan jusqu’à Bersabée, soixante dix mille hommes.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
Et, lorsque l’ange du Seigneur eut étendu sa main sur Jérusalem pour la détruire, le Seigneur eut pitié de son affliction, et dit à l’ange qui frappait le peuple: Il suffit, maintenant retiens ta main. Or, l’ange du Seigneur était alors près de l’aire d’Aréuna, le Jébuséen.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
Et David dit au Seigneur, quand il vit l’ange tuant le peuple: C’est moi qui ai péché et qui ai agi iniquement: ceux-ci, qui sont les brebis, qu’ont-ils fait? Que votre main, je vous conjure, se tourne contre moi et contre la maison de mon père.
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Or, Gad vint vers David en ce jour-là, et lui dit: Montez, et élevez au Seigneur un autel dans l’aire d’Aréuna, le Jébuséen.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
Et David monta selon la parole de Gad, que lui avait ordonnée le Seigneur.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Et regardant, Aréuna aperçut le roi et ses serviteurs venir vers lui;
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Et il sortit et se prosterna devant le roi, le visage incliné vers la terre, et il dit: Quelle raison y a-t-il pour que mon seigneur le roi vienne vers son serviteur? David lui répondit: C’est pour acheter de toi l’aire et bâtir un autel au Seigneur, afin que cesse la tuerie qui ravage le peuple.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Et Aréuna dit à David: Que mon seigneur le roi prenne, et qu’il offre comme il lui plaît: vous avez les bœufs pour l’holocauste, le char, et les jougs de bœufs, pour servir de bois.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Le roi Aréuna donna toutes ces choses au roi; et Aréuna dit au roi: Que le Seigneur votre Dieu reçoive votre vœu.
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Le roi, lui répondant, dit: Pas du tout comme vous voulez; mais j’achèterai de vous, selon le prix, et je n’offrirai point au Seigneur mon Dieu des holocaustes qui ne me coûtent rien. David donc acheta l’aire et les bœufs cinquante sicles d’argent.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Et David bâtit là un autel au Seigneur, et il offrit des holocaustes et des sacrifices pacifiques. Et le Seigneur devint propice à la terre, et la plaie fut écartée d’Israël.