< 2 Sama’ila 24 >
1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
Et de nouveau la colère de l'Éternel s'alluma contre les Israélites et excita David contre eux, en lui suggérant: Va, fais le recensement d'Israël et de Juda!
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Et le Roi dit à Joab, chef de la milice, à côté de lui: Fais donc la tournée de toutes les Tribus d'Israël de Dan à Béerseba, et passe le peuple en revue pour que j'en connaisse le chiffre.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Et Joab dit au Roi: Que non seulement l'Éternel, ton Dieu, ajoute au peuple, quelque nombreux qu'il soit, cent fois autant d'hommes, mais encore que les yeux de mon Seigneur le Roi en aient le spectacle! cependant pourquoi plaît-il au Roi, mon Seigneur, de prendre cette mesure?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Mais la parole du Roi prévalut sur Joab et sur les chefs militaires; et Joab et les chefs militaires sortirent, de l'audience du Roi pour passer le peuple d'Israël en revue.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Et ils traversèrent le Jourdain, et ils eurent leur quartier général vers Aroër à droite de la ville sise au milieu du ravin de Gad et dans la direction de Jaëzer.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Et ils gagnèrent Galaad et la terre neuve des habitants du Bas; et ils gagnèrent Dan-Jaan et les alentours du côté de Sidon;
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
et ils gagnèrent la place forte de Tyr et toutes les villes des Hévites et des Cananéens, et ils pénétrèrent au Midi de Juda vers Béerseba.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Ils parcoururent ainsi la totalité du pays, et ils rentrèrent à Jérusalem au bout de neuf mois et vingt jours.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Alors Joab présenta au Roi le résultat du recensement du peuple, et en Israël il y avait huit cent mille soldats tirant l'épée, et les hommes de Juda étaient au nombre de cinq cent mille.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Et David eut des remords en son cœur après qu'il eut fait le recensement du peuple, et David dit à l'Éternel: J'ai péché grandement par cet acte! Et maintenant, Éternel, veuille pardonner la faute de ton serviteur, car j'ai très follement agi!
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Et au lever de David le lendemain, la parole de l'Éternel fut adressée à Gad, le prophète, le Voyant de David, en ces termes:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Va et porte à David ces paroles: Ainsi parle l'Éternel: Je suspends sur toi trois menaces; choisis-en une, afin que je l'exécute.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Gad se présenta donc chez David et le mit au fait et lui dit: Veux-tu essuyer sept années de famine dans ton pays, ou bien fuir durant trois mois devant tes ennemis et être poursuivi par eux, ou bien avoir trois jours la peste dans ton pays? Maintenant réfléchis et vois quelle réponse je rendrai à Celui qui me délègue!
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
Alors David dit à Gad: Je suis dans une grande perplexité!… oh! tombons entre les mains de l'Éternel, car sa miséricorde est immense, mais que je ne tombe pas entre les mains des hommes!
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
Là-dessus l'Éternel envoya une peste en Israël depuis le matin jusqu'au terme fixé, et dans le peuple il mourut de Dan à Béerseba soixante-dix mille hommes.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
Et comme l'Ange étendait sa main sur Jérusalem pour la ravager, l'Éternel eut regret du fléau, et Il dit à l'Ange qui sévissait parmi le peuple: Assez! à présent ramène ta main! Or l'Ange de l'Éternel se trouvait alors près de l'aire d'Aravena, le Jébusite.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
Et David s'adressa à l'Éternel, lorsqu'il vit l'Ange taillant parmi le peuple, et dit: Voici, j'ai péché, et c'est moi qui suis en faute; mais ceux-là, ce troupeau, qu'ont-ils fait? que ta main fonde donc sur moi et la maison de mon père!
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Alors ce jour même, Gad arriva chez David et lui dit: Monte et érige à l'Éternel un autel sur l'aire d'Aravena, le Jébusite.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
Et David s'y rendit ensuite de la parole de Gad conforme à l'ordre de l'Éternel.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Et Aravena, qui regardait au dehors, vit le Roi et ses serviteurs se dirigeant vers lui; alors Aravena sortit, et il s'inclina devant le Roi, le visage contre terre.
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Et Aravena dit: Dans quel but mon Seigneur le Roi vient-il trouver son serviteur? Et David dit: Dans le but d'acheter de toi l'aire pour y bâtir un autel à l'Éternel, afin d'arrêter le fléau et d'en délivrer le peuple.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Et Aravena dit à David: Que mon Seigneur le Roi la prenne et fasse le sacrifice qu'il trouvera bon! vois! l'attelage servira pour l'holocauste et les traîneaux et les jougs des taureaux pour le bûcher.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
O Roi, Aravena fait don du tout au Roi. Et Aravena dit au Roi: Que l'Éternel, ton Dieu, te soit propice!
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Et le Roi dit à Aravena: Non, car je veux l'acheter de toi pour un prix, et je ne veux pas offrir à l'Éternel, mon Dieu, un sacrifice qui ne me coûte rien. David acheta donc l'aire et les taureaux pour cinquante sicles d'argent.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Et David y éleva un autel à l'Éternel, et offrit des holocaustes et des sacrifices pacifiques, et l'Éternel se laissa fléchir en faveur du pays, et le fléau fut détourné d'Israël.