< 2 Sama’ila 24 >

1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
Or la colère de l'Eternel s'embrasa encore contre Israël; parce que David fut incité contr'eux à dire: Va, dénombre Israël et Juda.
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Le Roi donc dit à Joab, chef de l'armée, lequel il avait avec soi: Passe maintenant par toutes les Tribus d'Israël, depuis Dan jusqu'à Beersébah, et dénombre le peuple, afin que j'en sache le nombre.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Mais Joab répondit au Roi: Que l'Eternel ton Dieu veuille augmenter ton peuple autant, et cent fois autant qu'il est maintenant; et que les yeux du Roi mon Seigneur le voient! mais pourquoi le Roi mon Seigneur prend-il plaisir à cela?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Néanmoins la parole du Roi l'emporta sur Joab, et sur les Chefs de l'armée; et Joab et les chefs de l'armée sortirent de la présence du Roi pour dénombrer le peuple, [savoir] Israël.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Ils passèrent donc le Jourdain, et se campèrent en Haroher, à main droite de la ville, qui est au milieu du torrent de Gad, et vers Jahzer.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Et ils vinrent en Galaad, et dans la terre de ceux qui habitent au bas [pays] d'Hodsi, et vinrent à Dan-Jahan, et ensuite aux environs de Sidon.
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Et ils vinrent jusqu'à la forteresse de Tsor, et dans toutes les villes des Héviens, et des Cananéens, et sortirent vers le Midi de Juda à Beersébah.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Ainsi ils traversèrent tout le pays, et revinrent à Jérusalem au bout de neuf mois et vingt jours.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Et Joab donna au Roi le rolle du dénombrement du peuple; et il y eut de ceux d'Israël huit cent mille hommes de guerre tirant l'épée, et de ceux de Juda cinq cent mille hommes.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Alors David fut touché en son cœur, après qu'il eut fait ainsi dénombrer le peuple; et David dit à l'Eternel: J'ai commis un grand péché en faisant cela, mais, je te prie, ô Eternel! pardonne l'iniquité de ton serviteur; car j'ai agi très-follement.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Après cela David se leva dès le matin, et la parole de l'Eternel fut [adressée] à Gad le Prophète, qui était le Voyant de David, en disant:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Va, et dis à David: Ainsi a dit l'Eternel: J'apporte trois choses contre toi; choisis l'une des trois, afin que je te la fasse.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Gad vint donc vers David, et lui fit entendre cela en disant: Que veux-tu qui t'arrive: ou sept ans de famine sur ton pays; ou que durant trois mois tu fuies devant tes ennemis, et qu'ils te poursuivent; ou que durant trois jours la mortalité soit en ton pays? Avises-y maintenant, et regarde ce que tu veux que je réponde à celui qui m'a envoyé.
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
Et David répondit à Gad: Je suis dans une très-grande angoisse. Je te prie que nous tombions entre les mains de l'Eternel, car ses compassions sont en grand nombre; et que je ne tombe point entre les mains des hommes.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
L'Eternel donc envoya la mortalité en Israël, depuis le matin jusqu'au temps de l'assignation; et il mourut du peuple depuis Dan jusqu'à Beersébah, soixante-dix mille hommes.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
Mais quand l'Ange eut étendu sa main sur Jérusalem pour la ravager, l'Eternel se repentit de ce mal-là et dit à l'Ange qui faisait le dégât parmi le peuple: C'est assez, retire à cette heure ta main. Or l'Ange de l'Eternel était auprès de l'aire d'Arauna Jébusien.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
Car David voyant l'Ange qui frappait le peuple, parla à l'Eternel, et dit: Voici, c'est moi qui ai péché, c'est moi qui ai commis l'iniquité, mais ces brebis qu'ont-elles fait? Je te prie que ta main soit contre moi, et contre la maison de mon père.
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Et en ce jour-là Gad vint vers David, et lui dit: Monte, et dresse un autel à l'Eternel dans l'aire d'Arauna Jébusien.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
Et David monta selon la parole de Gad, ainsi que l'Eternel l'avait commandé.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Et Arauna regarda, et vit le Roi, et ses serviteurs qui venaient vers lui; et ainsi Arauna sortit, et se prosterna devant le Roi, le visage contre terre.
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Et Arauna dit: Pour quel sujet le Roi mon Seigneur vient-il vers son serviteur? Et David répondit: Pour acheter ton aire, et y bâtir un autel à l'Eternel, afin que cette plaie soit arrêtée de dessus le peuple.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Et Arauna dit à David: Que le Roi mon Seigneur prenne et offre ce qu'il lui plaira. Voilà des bœufs pour l'holocauste, et des chariots, et un attelage de bœufs au lieu de bois.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Arauna donna tout cela au Roi [comme] un Roi. Et Arauna dit au Roi: L'Eternel ton Dieu veuille t'avoir pour agréable!
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Et le Roi répondit à Arauna: Non, mais je l'achèterai de toi pour un certain prix, et je n'offrirai point à l'Eternel mon Dieu des holocaustes qui ne me coûtent rien. Ainsi David acheta l'aire, et il [acheta aussi] les bœufs cinquante sicles d'argent.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Puis David bâtit là un autel à l'Eternel, et offrit des holocaustes et des sacrifices de prospérités; et l'Eternel fut apaisé envers le pays, et la plaie fut arrêtée en Israël.

< 2 Sama’ila 24 >