< 2 Sama’ila 24 >
1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
La colère du Seigneur s'enflamma encore contre Israël; et il poussa David contre le peuple, en lui disant: Va, et fais le dénombrement d'Israël et de Juda.
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Et le roi dit à Joab, général de ses troupes, qui était avec lui: Parcours toutes les tribus d'Israël et de Juda, depuis Dan jusqu'à Bersabée; fais le recensement du peuple, et j'en saurai le nombre.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Joab répondit au roi: Puisse le Seigneur Dieu ajouter à ce peuple, et le rendre cent fois aussi nombreux qu'il l'est; puisse le roi mon maître le voir de ses yeux; mais pourquoi le roi mon maître a-t-il formé ce dessein?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Mais la volonté du roi prévalut sur Joab et les autres chefs de l'armée. Joab partit donc avec les chefs des forces qui entouraient David, pour faire le recensement du peuple d'Israël.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Et ils traversèrent le Jourdain, et ils campèrent dans les champs d'Aroer, à droite de la ville, au milieu de la gorge de Gad et d'Eliézer.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Ils allèrent ensuite en Galaad et dans la terre de Thabason, la même qu'Adasaï; ils passèrent par Danidan, par Udan, et ils firent le tour de Sidon.
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Puis, ils allèrent à Mapsar de Tyr, et dans toutes les villes de l'Evéen et du Chananéen; et ils retournèrent au sud de Juda en Bersabée.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Et ils parcoururent toute la terre; enfin, ils rentrèrent à Jérusalem au bout de neuf mois et vingt jours.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Et Joab remit au roi le dénombrement du peuple qu'il avait recensé. Il y avait en Israël huit cent mille hommes dans la force de l'âge, portant l'épée, et en Juda cinq cent mille combattants.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Et le cœur de David le tourmenta, après qu'il eut compté le peuple, et il dit au Seigneur: J'ai gravement péché en ce que je viens de faire, ô Seigneur; remettez à votre serviteur son iniquité, car j'ai commis une insigne folie.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Et David se leva de grand matin, et la parole du Seigneur vint à Gad le voyant, le prophète, et le Seigneur lui dit:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Va, et parle à David, disant: Voici ce que dit le Seigneur: Je t'apporte trois choses: choisis pour toi l'une d'elles, et tu l'auras.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Et Gad entra chez le roi, lui parla, et lui dit: Choisis pour toi ce que tu veux qui arrive; il y aura ou trois années de famine en ta terre, ou trois mois, pendant lesquels tu fuiras devant tes ennemis qui te poursuivront, ou trois jours de mortalité dans ton royaume. Réfléchis, et vois ce que je dois répondre à Celui qui m'envoie.
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
Et David dit à Gad: De toutes parts le choix m'est cruel; mais j'aime mieux me livrer aux mains du Seigneur, parce qu'il a eu souvent compassion de moi; je ne tomberai point dans les mains des hommes.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
David choisit donc la mortalité; or, on était au temps de la moisson; et le Seigneur envoya la mort en Israël depuis le point du jour jusqu'à midi; la peste commença à frapper le peuple, et, de Dan à Bersabée, soixante-dix mille hommes périrent.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
Et l'ange de Dieu étendit la main sur Jérusalem pour la détruire; mais le Seigneur eut compassion de ses maux, et il dit à l'ange exterminateur qui détruisait le peuple: C'est assez, arrête ta main. Or, l'ange du Seigneur était auprès de l'aire d'Orna le Jébuséen.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
David, quand il vit l'ange du Seigneur frapper le peuple, parla au Seigneur, et lui dit: Me voici, c'est moi qui ai péché; mais ces brebis qu'ont-elles fait? Que votre main soit contre moi et contre la maison de mon père.
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Et ce jour-là, Gad vint à David, et il lui dit: Lève-toi, et dresse un autel au Seigneur dans l'aire d'Orna le Jébuséen.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
Et David se leva, comme le lui prescrivait Gad, et comme à Gad l'avait prescrit le Seigneur.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Orna était penché à sa fenêtre, et voyant le roi qui venait à lui avec ses serviteurs, il sortit, se prosterna devant le roi la face contre terre,
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Et dit: Pourquoi le roi mon maître est-il venu chez son serviteur? David répondit: C'est pour t'acheter ton aire, et y bâtir un autel au Seigneur, afin que cette peste cesse d'atteindre le peuple.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Et Orna dit à David: Que le roi mon maître prenne et consacre ce que bon lui semble; voici mes bœufs pour l'holocauste; les jougs et le chariot serviront à les brûler.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Ainsi, Orna donna tout au roi, et il lui dit: Que le Seigneur ton Dieu te bénisse.
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Mais le roi repartit: Je n'accepte point, je t'achèterai ce que tu m'offres, moyennant un bon prix; je ne présenterai point au Seigneur un holocauste qui ne me coûte rien. Et David acheta l'aire avec les bœufs cinquante sicles d'argent.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Aussitôt, David bâtit l'autel au Seigneur; puis, il y offrit des holocaustes et des hosties pacifiques. Salomon embellit plus tard l'autel, qui était d'abord fort petit. Pour le moment, le Seigneur exauça les vœux de la terre, et la peste cessa en Israël.