< 2 Sama’ila 24 >

1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
La colère de Yahweh s'enflamma de nouveau contre Israël, et il excita David contre eux, en disant: « Va, fais le dénombrement d'Israël et de Juda. »
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Le roi dit à Joab, chef de l'armée, qui était avec lui: « Parcours donc toutes les tribus d'Israël, depuis Dan jusqu'à Bersabée; faites le dénombrement du peuple, afin que je sache le chiffre du peuple. »
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Joab dit au roi: « Que Yahweh ton Dieu ajoute au peuple cent fois ce qu'il y en a, et que les yeux du roi mon seigneur le voient! Mais pourquoi le roi mon seigneur met-il son plaisir à faire cela? »
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
Mais la parole du roi prévalut contre Joab, et sur les chefs de l'armée; et Joab et les chefs de l'armée partirent de devant le roi pour faire le dénombrement du peuple d'Israël.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
Ayant passé le Jourdain, ils campèrent à Aroër, à droite de la ville, qui est au milieu de la vallée de Gad, puis à Jazer.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Ils vinrent en Galaad et dans le pays de Thachthim-Hodsi; puis ils vinrent à Dan-Jaan et aux environs de Sidon.
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Ils vinrent à la place forte de Tyr et dans toutes les villes des Hévéens et des Chananéens, ils aboutirent au Négeb de Juda, à Bersabée.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
Lorsqu'ils eurent ainsi parcouru tout le pays, ils revinrent à Jérusalem au bout de neuf mois et vingt jours.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
Joab remit au roi le rôle du dénombrement du peuple: il y avait en Israël huit cent mille hommes de guerre tirant l'épée, et en Juda cinq cent mille hommes.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
David sentit battre son cœur après qu'il eut compté le peuple, et David dit à Yahweh: « J'ai commis un grand péché en ce que j'ai fait! Maintenant, ô Yahweh, ôtez, je vous prie, l'iniquité de votre serviteur, car j'ai tout à fait agi en insensé. »
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Le lendemain, quand David se leva, la parole de Yahweh fut adressée à Gad, le prophète, le voyant de David, en ces termes:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
« Va dire à David: Ainsi parle Yahweh: Je mets devant toi trois choses; choisis-en une, et je te la ferai. »
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Gad vint vers David et lui fit connaître la parole de Yahweh, et lui dit: « Une famine de sept années viendra-t-elle dans ton pays, ou bien fuiras-tu trois mois devant tes ennemis qui te poursuivront, ou bien y aura-t-il une peste de trois jours dans ton pays? Maintenant, sache et vois ce que je dois répondre à celui qui m'envoie. »
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
David répondit à Gad: « Je suis dans une cruelle angoisse. Ah! Tombons entre les mains de Yahweh, car ses miséricordes sont grandes; mais que je ne tombe pas entre les mains des hommes! »
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
Et Yahweh envoya une peste en Israël depuis le matin de ce jour jusqu'au temps fixé; et il mourut, de Dan à Bersabée, soixante-dix mille hommes parmi le peuple.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
L'ange étendait la main sur Jérusalem pour la détruire. Et Yahweh se repentit de ce mal, et il dit à l'ange qui faisait périr le peuple: « Assez! retire maintenant ta main. » L'ange de Yahweh se tenait près de l'aire d'Areuna, le Jébuséen.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
A la vue de l'ange qui frappait le peuple, David dit à Yahweh: « Voici, c'est moi qui ai péché, c'est moi qui suis coupable; mais celles-là, ces brebis, qu'ont-elles fait? Que ta main soit donc sur moi et sur la maison de mon père! »
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Ce jour-là, Gad vint auprès de David et lui dit: « Monte et élève à Yahweh un autel sur l'aire d'Areuna, le Jébuséen. »
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
David monta, selon la parole de Gad, comme Yahweh l'avait ordonné.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
Areuna, ayant regardé, vit le roi et ses serviteurs qui se dirigeaient vers lui;
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
Areuna sortit et se prosterna devant le roi, le visage contre terre, en disant: « Pourquoi mon seigneur le roi vient-il vers son serviteur? » Et David répondit: « Pour acheter de toi cette aire afin de bâtir un autel à Yahweh, pour que la plaie se retire de dessus le peuple. »
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Areuna dit à David: « Que mon seigneur le roi prenne l'aire et qu'il offre en sacrifice ce qu'il trouvera bon! Voici les bœufs pour l'holocauste, les traîneaux et les jougs des bœufs pour le bois.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Tout cela, ô roi, Areuna le donne au roi. » Et Areuna dit encore au roi: « Que Yahweh; ton Dieu, te sois favorable! »
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Mais le roi dit à Areuna: « Non! Mais je veux l'acheter de toi à prix d'argent, et je n'offrirai point à Yahweh, mon Dieu, des holocaustes qui ne me coûtent rien. » Et David acheta l'aire et les bœufs pour cinquante sicles d'argent.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
Et David bâtit là un autel à Yahweh et offrit des holocaustes et des sacrifices pacifiques. Ainsi Yahweh fut apaisé envers le pays, et la plaie se retira d'Israël.

< 2 Sama’ila 24 >