< 2 Sama’ila 24 >
1 Fushin Ubangiji ya sāke ƙuna a kan Isra’ila, sai ya zuga Dawuda, yana cewa, “Je ka ƙidaya Isra’ila da Yahuda.”
Tedy opět prchlivost Hospodinova popudila se proti Izraelovi; nebo byl ponukl satan Davida na ně, řka: Jdi, sečti lid Izraelský a Judský.
2 Saboda haka sarki ya ce wa Yowab da komandodin da suke tare da shi, “Tafi cikin dukan kabilan Isra’ila, daga Dan har zuwa Beyersheba, ku ƙidaya mayaƙa don in san yawansu.”
Protož řekl král Joábovi, hejtmanu vojska svého: Projdi i hned všecka pokolení Izraelská od Dan až k Bersabé, a sečtěte lid, abych věděl počet jeho.
3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mayaƙan su ƙaru sau ɗari fiye da yadda suke, har ranka yă daɗe, sarki yă gani da idonsa. Me ya sa ranka yă daɗe, sarki yake so yă yi abu haka?”
Ale Joáb řekl králi: Přidejž Hospodin Bůh tvůj k lidu, jakž ho koli mnoho, stokrát více, a to aby oči pána mého krále viděly. Ale proč pán můj král jest toho tak žádostiv?
4 Duk da haka, maganar sarki ya rinjayi Yowab da komandodin soja, sai suka tashi daga gaban sarki, suka tafi su ƙirga mayaƙan Isra’ila.
A však přemohla řeč králova Joába i knížata vojska. Protož vyšel Joáb a knížata vojska od tváři královy, aby sečtli lid Izraelský.
5 Bayan suka ƙetare Urdun, sai suka yi sansani kusa da Arower, kudu da garin da yake cikin kwari, sa’an nan suka ratsa ta wajen Gad, suka ci gaba zuwa Yazer.
A přepravivše se přes Jordán, položili se při Aroer po pravé straně města, kteréž jest u prostřed potoka Gád, a při Jazer.
6 Suka tafi Gileyad ta yankin Tatim Hodshi, sa’an nan suka tafi Dan Ya’an, suka kuma yi wajen kewaye Sidon.
Potom přišli do Galád a do země dolejší nové, odkudž šli do Dan Jáhan a do okolí Sidonského.
7 Sa’an nan suka yi ta wajen kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa da Kan’aniyawa. A ƙarshe, suka ci gaba zuwa Beyersheba a Negeb na Yahuda.
Přišli také ku pevnosti Týru, a ke všem městům Hevejských a Kananejských; odkudž šli na poledne země Judské do Bersabé.
8 Bayan suka ratsa dukan ƙasashen, a ƙarshe suka koma Urushalima, bayan wata tara da kwana ashirin.
A když schodili všecku zemi, přišli po přeběhnutí devíti měsíců a dvadcíti dní do Jeruzaléma.
9 Yowab ya ba wa sarki jimillar yawan mayaƙan. A Isra’ila akwai mutum dubu ɗari takwas da za su iya riƙe takobi. A Yahuda kuwa mutum dubu ɗari biyar.
I dal Joáb počet sečteného lidu králi. Bylo pak lidu Izraelského osmkrát sto tisíc mužů silných, kteříž mohli vytrhnouti meč k bitvě. Mužů také Judských pětkrát sto tisíc.
10 Bayan Dawuda ya ƙidaya mayaƙan, lamirinsa ya kāshe shi, sai ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka ka gafarta wa bawanka. Na yi wauta ƙwarai.”
Potom padlo to těžce na srdce Davidovi, když již sečtl lid. I řekl David Hospodinu: Zhřešilť jsem těžce, že jsem to učinil, ale nyní, ó Hospodine, odejmi, prosím, nepravost služebníka svého, nebť jsem velmi bláznivě učinil.
11 Kafin Dawuda yă tashi da safe kashegari, maganar Ubangiji ta riga ta zo wa annabin nan Gad, mai duban nan na Dawuda. Ubangiji ya ce,
Když pak vstal David ráno, stalo se slovo Hospodinovo k Gádovi proroku, vidoucímu Davidovu, řkoucí:
12 “Je ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, ina ba ka zaɓi uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata maka shi.’”
Jdi a rci Davidovi: Toto praví Hospodin: Trojíť věci podávám, vyvol sobě jednu z nich, kteroužť bych učinil.
13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gābanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu, sai ka yi tunani, ka yanke shawarar game da amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.”
Protož přišed Gád k Davidovi, oznámil mu to, a řekl jemu: Chceš-li, aby přišel na tebe hlad za sedm let v zemi tvé? čili abys za tři měsíce utíkal před nepřátely svými, a oni aby tě honili? čili aby za tři dni byl mor v zemi tvé? Pomysliž spěšně, a viz, jakou mám odpověd dáti tomu, kterýž mne poslal.
14 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Gara mu fāɗa a hannuwan Ubangiji gama alherinsa da girma yake. Amma fa kada ka bar ni in fāɗa a hannun mutane.”
I řekl David k Gádovi: Úzkostmi sevřín jsem náramně; nechať, prosím, upadneme v ruku Hospodinovu, neboť jsou mnohá slitování jeho, jediné ať v ruce lidské neupadám.
15 Saboda haka Ubangiji ya aika da annoba a kan Isra’ila tun daga safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade, mutum dubu saba’in kuwa daga Dan zuwa Beyersheba suka mutu.
A tak uvedl Hospodin mor na Izraele od jitra až do času uloženého, a zemřelo jich z lidu od Dan až do Bersabé sedmdesáte tisíc mužů.
16 Da mala’ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima, don yă hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala’ikan da yake wahal da mutane, “Ya isa, ka janye hannunka.” A lokacin kuwa Mala’ikan Ubangiji yana tsaye a masussukar Arauna, mutumin Yebus.
A když vztáhl anděl ruku svou na Jeruzalém, aby hubil jej, litoval Hospodin toho zlého, a řekl andělu, kterýž hubil lid: Dostiť jest, již přestaň. Anděl pak Hospodinův byl u humna Aravny Jebuzejského.
17 Da Dawuda ya ga mala’ikan da ya bubbugi mutane, sai ya ce wa Ubangiji, “Ni ne na yi zunubi, na kuma yi abin da ba daidai ba. Waɗannan tumaki ne kawai. Me suka yi? Bari hukuncinka yă sauko a kaina da iyalina.”
I mluvil David Hospodinu, když uzřel anděla, an bije lid, a řekl: Aj, já jsem zhřešil, a já jsem neprávě učinil, ale tito, jsouce jako ovce, co učinili? Nechť jest, prosím, ruka tvá proti mně a proti domu otce mého.
18 A ranar, Gad ya koma wurin Dawuda ya ce, “Ka tashi, ka tafi ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna, mutumin Yebus.”
Potom navrátiv se Gád k Davidovi v ten den, řekl jemu: Vstup a vzdělej Hospodinu oltář na humně Aravny Jebuzejského.
19 Saboda haka Dawuda ya haura, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Gad.
I šel David vedlé řeči Gádovy, jakož byl přikázal Hospodin.
20 Da Arauna ya hangi Dawuda da mutanensa suna zuwa wajensa, sai ya fita a guje, ya je ya rusuna a gaban sarki.
A vyhlédaje Aravna, uzřel krále s služebníky jeho, an jdou k němu; protož vyšed Aravna, poklonil se králi tváří svou až k zemi.
21 Arauna ya ce, “Me ya sa ranka yă daɗe, sarki ya zo wajen bawansa?” Dawuda ya ce, “Don in saya masussukarka, saboda in gina wa Ubangiji bagade don a tsayar da annoban da suke a bisa mutane.”
I řekl Aravna: Proč přišel pán můj král k služebníku svému? Odpověděl David: Abych koupil od tebe humno toto, na němž bych vzdělal oltář Hospodinu, aby přestala rána tato v lidu.
22 Arauna ya ce wa Dawuda, “Bari ranka yă daɗe, sarki yă ɗauki duk abin da ya ga dama yă miƙa shi. Ga shanu, don hadaya ta ƙonawa, ga kuma kayan masussuka da itacen shanu, don itace.”
Opět řekl Aravna Davidovi: Nechť vezme a obětuje pán můj král, což se mu za dobré vidí. Aj, teď volové k oběti zápalné, a smyky vozové i přípravy volů na drva.
23 Dukan wannan, ranka yă daɗe, Arauna ya ba wa sarki. Arauna ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahnka yă karɓa.”
Všecky ty věci dával králík Aravna králi. Řekl ještě Aravna králi: Hospodin Bůh tvůj zalibiž tě sobě.
24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A’a, dole in biya ka saboda waɗannan. Ba yadda zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da bai ci mini kome ba.” Sai Dawuda ya saya, ya kuma biya masussukar, da shanun a bakin shekel hamsin na azurfa.
Řekl pak král Aravnovi: Nikoli, ale raději koupím od tebe, a zaplatím, aniž budu obětovati Hospodinu Bohu svému oběti zápalné darem dané. A tak koupil David humno a voly za padesáte lotů stříbra.
25 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama. Sa’an nan Ubangiji ya amsa addu’o’in a madadin ƙasar, aka kuma kawar wa Isra’ila annoban.
A vzdělav tu David oltář Hospodinu, obětoval oběti zápalné a pokojné. I byl milostiv Hospodin zemi, a přestala zhouba v Izraeli.