< 2 Sama’ila 23 >

1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
Dessa voro Davids sista ord: Så säger David, Isais son, så säger den man som blev högt upphöjd, Jakobs Guds smorde, Israels ljuvlige sångare:
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
HERRENS Ande har talat genom mig, och hans ord är på min tunga;
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
Israels Gud har så sagt, Israels klippa har så talat till mig: "Den som råder över människorna rätt, den som råder i Guds fruktan,
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
han är lik morgonens ljus, när solen går upp, en morgon utan moln, då jorden grönskar genom solsken efter regn.
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
Ja, är det icke så med mitt hus inför Gud? Han har ju upprättat med mig ett evigt förbund, i allo stadgat och betryggat. Ja, visst skall han låta all frälsning och glädje växa upp åt mig.
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
Men de onda äro allasammans lika bortkastade törnen, som man ej vill taga i med handen.
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
Och måste man röra vid dem, så rustar man sig med järn och med spjutskaft, och bränner sedan upp dem i eld på stället.
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
Dessa äro namnen på Davids hjältar: Joseb-Bassebet, en takemonit, den förnämste bland kämparna, han som svängde sitt spjut över åtta hundra som hade blivit slagna på en gång.
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
Och näst honom kom Eleasar, son till Dodi, son till en ahoait. Han var en av de tre hjältar som voro med David, när de blevo smädade av filistéerna, som där hade församlat sig till strid; Israels män drogo sig då tillbaka.
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
Men han höll stånd och högg in på filistéerna, till dess att hans hand blev så trött att den var såsom faststelnad vid svärdet; och HERREN beredde så en stor seger på den dagen. Sedan hade folket allenast att vända om och följa med honom för att plundra.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
Och efter honom kom Samma, son till Age, en hararit. En gång hade filistéerna församlat sig, så att de utgjorde en hel skara. Och där var ett åkerstycke, fullt med linsärter. Och folket flydde för filistéerna.
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
Då ställde han sig mitt på åkerstycket och försvarade det och slog filistéerna; och HERREN beredde så en stor seger.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
En gång drogo tre av de trettio förnämsta männen ned och kommo vid skördetiden till David vid Adullams grotta, medan en skara filistéer var lägrad i Refaimsdalen.
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
Men David var då på borgen, under det att en filisteisk utpost fanns i Bet-Lehem.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
Och David greps av lystnad och sade: "Ack att någon ville giva mig vatten att dricka från brunnen vid Bet-Lehems stadsport!"
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
Då bröto de tre hjältarna sig igenom filistéernas läger och hämtade vatten ur brunnen vid Bet-Lehems stadsport och togo det och buro det till David. Men han ville icke dricka det, utan göt ut det såsom ett drickoffer åt HERREN.
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Han sade nämligen: "Bort det, HERRE, att jag skulle göra detta! Skulle jag dricka de mäns blod, som gingo åstad med fara för sina liv?" Och han ville icke dricka det. Sådana ting hade de tre hjältarna gjort.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
Abisai, broder till Joab, Serujas son, var den förnämste av tre andra; han svängde en gång sitt spjut över tre hundra som hade blivit slagna. Och han hade ett stort namn bland de tre.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Han var visserligen mer ansedd än någon annan i detta tretal, och han var de andras hövitsman, men upp till de tre första kom han dock icke.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
Och Benaja, son till Jojada, som var son till en tapper, segerrik man från Kabseel; han slog ned de två Arielerna i Moab, och det var han som en snövädersdag steg ned och slog ihjäl lejonet i brunnen.
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
Han slog ock ned den egyptiske mannen som var så ansenlig att skåda. Fastän egyptiern hade ett spjut i handen, gick han ned mot honom, väpnad allenast med sin stav. Och han ryckte spjutet ur egyptierns hand och dräpte honom med hans eget spjut.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
Sådana ting hade Benaja, Jojadas son, gjort. Och han hade ett stort namn bland de tre hjältarna.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
Han var mer ansedd än någon av de trettio, men upp till de tre första kom han icke. Och David insatte honom i sin livvakt.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
Till de trettio hörde: Asael, Joabs broder; Elhanan, Dodos son, från Bet-Lehem;
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
haroditen Samma; haroditen Elika;
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
peletiten Heles; tekoaiten Ira, Ickes' son;
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
anatotiten Abieser; husatiten Mebunnai;
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
ahoaiten Salmon; netofatiten Maherai;
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
netofatiten Heleb, Baanas son; Ittai, Ribais son, från Gibea i Benjamins barns stam;
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Benaja, en pirgatonit; Hiddai från Gaas' dalar;
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
arabatiten Abi-Albon; barhumiten Asmavet;
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
saalboniten Eljaba; Bene-Jasen; Jonatan;
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
harariten Samma; arariten Ahiam, Sarars son;
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Elifelet, son till Ahasbai, maakatitens son; giloniten Eliam, Ahitofels son;
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
Hesro från Karmel; arabiten Paarai;
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Jigeal, Natans son, från Soba; gaditen Bani;
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
ammoniten Selek; beerotiten Naharai, vapendragare åt Joab, Serujas son;
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
jeteriten Ira; jeteriten Gareb;
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
hetiten Uria. Tillsammans utgjorde de trettiosju.

< 2 Sama’ila 23 >