< 2 Sama’ila 23 >
1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
А ово су последње речи Давидове: Рече Давид син Јесејев, рече човек који би постављен високо, помазаник Бога Јаковљевог, и љубак у песмама Израиљевим:
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
Дух Господњи говори преко мене, и беседа Његова би на мом језику.
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
Рече Бог Израиљев, каза ми Стена Израиљева; који влада људима нека је праведан, владајући у страху Божијем;
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
И биће као светлост јутарња, кад сунце излази јутром без облака, и као трава која расте из земље од светлости иза дажда.
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
Ако и није такав дом мој пред Богом, ипак је учинио завет вечан са мном, у свему добро уређен и утврђен. И то је све спасење моје и сва жеља моја, ако и не да да расте.
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
А безаконици ће свиколики бити као трње почупани, које се не хвата руком.
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
Него ко хоће да га се дохвати, узме гвожђе или копљачу; и сажиже се огњем на месту.
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
Ово су имена јунака Давидових: Јосев-Васевет Тахмонац први између тројице; њему милина би ударити копљем на осам стотина и поби их уједанпут.
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
За њим Елеазар син Додона сина Ахоховог, између три јунака који беху с Давидом, и осрамотише Филистеје скупљене на бој, кад Израиљци отидоше;
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
Он се подиже, и би Филистеје докле му се рука не умори и укочи се при мачу: и Господ даде велико спасење онај дан, те се народ врати за њим само да покупи плен.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
А за њим Сама син Агејев Араранин; кад се Филистеји скупише у гомилу, и онде беше њива пуна лећа, и народ побеже од Филистеја,
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
Стаде усред њиве, и одбрани је, и поби Филистеје, и Бог даде велико спасење.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
И та три прва између тридесет сиђоше и дођоше о жетви к Давиду у пећину одоламску, кад војска филистејска стајаше у логору, у долини рафајској.
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
А Давид беше онда у граду, и беше онда стража филистејска у Витлејему.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
А Давид зажеле, и рече: Ко би ми донео воде да пијем из студенца витлејемског што је код врата!
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
Тада она три јунака продреше кроз логор филистејски, и захватише воде из студенца витлејемског што је код врата, и донесоше и дадоше Давиду; али он је не хте пити, него је проли пред Господом;
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
И рече: Не дај Боже да бих то учинио. Није ли то крв ових људи, који не марећи за живот свој идоше. И не хте пити. То учинише ова три јунака.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
И Ависај брат Јоавов син Серујин беше први између тројице; он махну копљем својим на три стотине, и поби их, и прослави се међу тројицом.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Између те тројице беше најславнији, и поста им поглавар; али оне тројице не стиже.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
И Венаја син Јодајев, син човека јунака, велик делима, из Кавсеила; он погуби два јунака моавска, и сишав уби лава у јами кад беше снег.
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
Он уби и једног Мисирца, знатног човека; имаше Мисирац копље у руци, а он изиђе на њ са штапом, и истрже Мисирцу копље из руке, и уби га његовим копљем.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
То учини Венаја син Јодајев, и би славан међу ова три јунака.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
Беше најславнији између тридесеторице, али оне тројице не стиже; и Давид га постави над пратиоцима својим.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
Асаило брат Јоавов беше међу тридесеторицом, а то беху: Елханан син Додонов из Витлејема,
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
Сама Арођанин, Елика Арођанин.
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
Хелис Фалћанин, Ира син Икисов Текујанин,
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
Авијезер Анатоћанин, Мевунеј Хусаћанин,
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
Салмон Ахошанин, Марај Нетофаћанин,
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
Хелев син Ванин Нетофаћанин, Итај син Ривајев из Гаваје синова Венијаминових,
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Венаја Пиротоњанин, Идај из долине Гаса.
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
Ави-Алвон Арваћанин, Азмавет Варумљанин,
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
Елијава Салвоњанин, Јонатан од синова Јасинових,
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
Сама Араранин, Ахијам син Сахаров Араранин,
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Елифелет, син Асвеја Махаћанина, Елијем син Ахитофела Гилоњанина.
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
Есрај Кармилац, Фареј Арвљанин,
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Игал син Натанов из Сове, Ванија од Гада,
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
Селек Амонац, Нареј Вироћанин, који ношаше оружје Јоаву сину Серујином,
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
Ира Јетранин, Гарив Јетранин,
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
Урија Хетејин; свега тридесет и седам.