< 2 Sama’ila 23 >

1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
Now estas são as últimas palavras de David. David, o filho de Jesse, diz, o homem que foi criado no alto diz, o ungido do Deus de Jacob, o doce salmista de Israel:
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
“O Espírito de Yahweh falou por mim. Sua palavra estava na minha língua.
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
Disse o Deus de Israel, a Rocha de Israel falou comigo, “Aquele que rege sobre os homens com retidão, que reina no temor de Deus,
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
será como a luz da manhã quando o sol nascer, uma manhã sem nuvens, quando a tenra grama brota da terra, através de um claro brilho após a chuva”.
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
Minha casa não é assim com Deus? No entanto, ele fez comigo um pacto eterno, encomendado em todas as coisas, e com certeza, pois é toda a minha salvação e todo o meu desejo. Ele não vai fazê-lo crescer?
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
Mas todos os ímpios serão como espinhos a serem empurrados para longe, porque elas não podem ser tomadas com a mão.
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
O homem que os toca deve estar armado com ferro e com o bastão de uma lança. Eles serão totalmente queimados com fogo em seu lugar”.
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
Estes são os nomes dos homens poderosos que David tinha: Josheb Basshebeth, um tahchemonita, chefe dos capitães; chamava-se Adino, o Eznite, que matou oitocentos de uma só vez.
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
Depois dele foi Eleazar, filho de Dodai, filho de um Ahohite, um dos três homens poderosos com Davi quando desafiaram os filisteus que estavam ali reunidos para a batalha, e os homens de Israel tinham ido embora.
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
Ele se levantou e atingiu os filisteus até que sua mão se cansou, e sua mão congelou até a espada; e Javé trabalhou uma grande vitória naquele dia; e o povo voltou atrás dele apenas para saquear.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
Depois dele foi Shammah, o filho de Agee a Hararite. Os filisteus tinham se reunido em uma tropa onde havia um terreno cheio de lentilhas; e o povo fugiu dos filisteus.
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
Mas ele ficou no meio da trama e a defendeu, e matou os filisteus; e Yahweh trabalhou uma grande vitória.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
Três dos trinta chefes desceram, e vieram a David na época da colheita para a caverna de Adullam; e a tropa dos filisteus estava acampada no vale de Rephaim.
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
David estava então na fortaleza; e a guarnição dos filisteus estava então em Belém.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
David disse longamente: “Oh, que alguém me desse água para beber do poço de Belém, que está junto ao portão”!
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
Os três poderosos atravessaram o exército dos filisteus e tiraram água do poço de Belém que estava junto ao portão e a levaram e trouxeram a Davi; mas ele não quis beber dela, mas derramou-a para Iavé.
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Ele disse: “Fique longe de mim, Yahweh, que eu deveria fazer isto! Não é este o sangue dos homens que arriscaram suas vidas para ir embora?”. Portanto, ele não o beberia. Os três homens poderosos fizeram estas coisas.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
Abishai, o irmão de Joab, filho de Zeruiah, era o chefe dos três. Ele ergueu sua lança contra trezentos e os matou, e tinha um nome entre os três.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Wasn ele não era o mais honrado dos três? Portanto, ele foi nomeado seu capitão. Entretanto, ele não foi incluído como um dos três.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
Benaiah, filho de Jehoiada, filho de um valente homem de Kabzeel, que tinha feito grandes feitos, matou os dois filhos de Ariel de Moab. Ele também desceu e matou um leão no meio de um poço em um tempo de neve.
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
Ele matou um egípcio enorme, e o egípcio tinha uma lança na mão; mas ele desceu até ele com um bastão e arrancou a lança da mão do egípcio, e o matou com sua própria lança.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
Benaiah, o filho de Jehoiada, fez estas coisas e tinha um nome entre os três homens poderosos.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
Ele era mais honrado do que os trinta, mas não chegou aos três. David o colocou por cima de sua guarda.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
Asahel, irmão de Joab, era um dos trinta: Elhanan o filho de Dodo de Belém,
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
Shammah o Harodita, Elika o Harodita,
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
Helez o Paltita, Ira o filho de Ikkesh o Tekoite,
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
Abiezer o Anatotita, Mebunnai o Hushathite,
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
Zalmon o Ahohite, Maharai o Netophathite,
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
Heleb o filho de Baanah o Netophathite, Ittai o filho de Ribai de Gibeah dos filhos de Benjamin,
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Benaiah a Pirathonite, Hiddai dos riachos de Gaash.
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
Abialbon o arbatita, Azmaveth o barhumita,
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
Eliahba o saalbonita, os filhos de Jashen, Jonathan,
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
Shammah o hararita, Ahiam o filho de Sharar o ararita,
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Elifelet o filho de Ahasbai, o filho do maacatita, Eliam o filho de Ahithophel o gilonita,
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
Hezro o Carmelita, Paarai o Árbitro,
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Igal o filho de Nathan de Zobah, Bani o Gadita,
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
Zelek o Amonita, Naharai o Beerotita, portadores de armadura para Joab o filho de Zeruia,
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
Ira o Ítrito, Gareb o Ítrito,
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
e Uriah o Hitita: trinta e sete no total.

< 2 Sama’ila 23 >