< 2 Sama’ila 23 >
1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
Now these are the last words of David— David son of Jesse, the man who was highly honored, the one anointed by the God of Jacob, the sweet psalmist of Israel.
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
“The Spirit of Yahweh spoke by me, and his word was on my tongue.
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
The God of Israel spoke, the Rock of Israel said to me, 'The one who rules righteously over men, who rules in the fear of God.
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
He will be like the morning light when the sun rises, a morning without clouds, when the tender grass springs up from the earth through bright sunshine after rain.
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
Indeed, is my family not like this before God? Has he not made an everlasting covenant with me, ordered and sure in every way? Does he not increase my salvation and fulfill my every desire?
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
But the worthless will all be like thorns to be thrown away, because they cannot be gathered by one's hands.
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
The man who touches them must use an iron tool or the shaft of a spear. They must be burned up where they lie.'”
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
These are the names of David's mighty men: Jeshbaal the Hachmonite was the leader of the mighty men. He killed eight hundred men on one occasion.
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
After him was Eleazar son of Dodai the Ahohite, one of the three mighty men. He was with David when they taunted the Philistines who had gathered together to do battle, and when the men of Israel had retreated.
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
Eleazar stood and fought the Philistines until his hand became weary and his hand stiffened to the grip of his sword. Yahweh brought about a great victory that day. The army returned after Eleazar, only to strip the bodies.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
After him was Shammah son of Agee, a Hararite. The Philistines gathered together where there was a field of lentils, and the army fled from them.
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
But Shammah stood in the middle of the field and defended it. He killed the Philistines, and Yahweh brought about a great victory.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
Three of the thirty soldiers went down to David at harvest time, to the cave of Adullam. The army of the Philistines was camped in the Valley of Rephaim.
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
At that time David was in his stronghold, a cave, while the Philistines had established at Bethlehem.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
David was longing for water and said, “If only someone would give me water to drink from the well at Bethlehem, the well that is by the gate!”
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
So these three mighty men broke through the army of the Philistines and drew water out of the well of Bethlehem, the well at the gate. They took the water and brought it to David, but he refused to drink it. Instead, he poured it out to Yahweh.
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Then he said, “Yahweh, far be it from me, that I should do this. Should I drink the blood of men who have risked their lives?” So he refused to drink it. These things were done by the three mighty.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
Abishai, brother of Joab and son of Zeruiah, was captain over the three. He once fought with his spear against three hundred men and killed them. He was often mentioned along with the three soldiers.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Was he not even more famous than the three? He was made their captain. However, his fame did not equal the fame of the three most famous soldiers.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
Benaiah from Kabzeel was the son of Jehoiada; he was a strong man who did mighty feats. He killed the two sons of Ariel of Moab. He also went down into a pit and killed a lion while it was snowing.
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
Then he killed a very large Egyptian man. The Egyptian had a spear in his hand, but Benaiah fought against him with only a staff. He seized the spear out of the Egyptian's hand and then killed him with his own spear.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
Benaiah son of Jehoiada did these feats, and he was named alongside the three mighty men.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
He was more highly regarded than the thirty soldiers in general, but he was not regarded quite as highly as the three mighty men. Yet David put him in charge of his bodyguard.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
The thirty included the following men: Asahel brother of Joab, Elhanan son of Dodo from Bethlehem,
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
Shammah the Harodite, Elika the Harodite,
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
Helez the Paltite, Ira son of Ikkesh the Tekoite,
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
Abiezer the Anathothite, Sibbekai the Hushathite,
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
Zalmon the Ahohite, Maharai the Netophathite;
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
Heleb son of Baanah, the Netophathite, Ithai son of Ribai from Gibeah of the Benjamites,
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Benaiah the Pirathonite, Hiddai of the valleys of Gaash.
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
Abi-Albon the Arbathite, Azmaveth the Barhumite,
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
Eliahba the Shaalbonite, the sons of Jashen, Jonathan son of Shammah the Hararite;
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
Ahiam son of Sharar the Hararite,
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Eliphelet son of Ahasbai the Maakathite, Eliam son of Ahithophel the Gilonite,
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
Hezro the Carmelite, Paarai the Arbite,
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Igal son of Nathan from Zobah, Bani from the tribe of Gad,
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
Zelek the Ammonite, Naharai the Beerothite, armor bearer to Joab son of Zeruiah,
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
Ira the Ithrite, Gareb the Ithrite,
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
Uriah the Hittite—thirty-seven in all.