< 2 Sama’ila 23 >

1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
David, the son of Jesse, was a man whom [God caused to] become great. He was appointed to become king by the God whom Jacob [worshiped]. He wrote beautiful songs for the Israeli people. This is the last song that he wrote:
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
“The Spirit of Yahweh tells me what to say; the message that I speak [MTY] comes from him.
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
God, the one whom we Israeli [people worship], has spoken; the one who protects us Israeli people said to me, ‘Kings who rule people justly have an awesome respect for me, God.
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
They are like the sun that shines at dawn and causes the grass to [sprout/sparkle] after the rain ends.’
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
And truly, that is how God will surely bless my family [RHQ] because he made an agreement with me that will endure forever, an agreement in which he promises that no part of it will ever be changed. He will surely cause me to prosper [RHQ], and he will always help me, and that is all that I desire.
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
But [he will get rid of] godless/evil people like [SIM] people throw away thorns that [injure people if they try to] pick them up with their hands.
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
Someone [who wants to get rid of thornbushes] does not grab them; he uses an iron [shovel] or a spear [to dig them out] and then he burns them completely.
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
These are the names of David’s three greatest warriors. The first was Esh-Baal, [whose other name was Jashobeam], from the Hachmon clan (OR, the son of Hachmon). He was the leader of the three men. One time he fought against 800 enemies and killed them all with his spear.
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
The second/next one of the three greatest warriors was Eleazar, who was the son of Dodo from the clan of Ahoh. One day he was with David when they defied/challenged the soldiers of Philistia who had gathered for the battle. The [other] Israeli soldiers retreated,
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
but Eleazar stood there and fought the soldiers of Philistia until his arm became very tired, with the result that [his hand cramped and] he could not stop gripping his sword. Yahweh won a great victory on that day. And afterwards the [other] Israeli soldiers returned [to where Eleazar was], and stripped off the [armor from the men whom he had] killed.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
The third one of the greatest warriors was Shammah, the son of Agee from [the clan/town of] Harar. One time the Philistia soldiers gathered at Lehi [town], where there was a field full of lentils/peas [that they wanted to steal]. The other Israeli soldiers ran away from the Philistia troops,
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
but Shammah stood there in the field and did not let the Philistia soldiers [steal the crops], and killed them. Yahweh won a great victory on that day.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
Altogether there were 30 special warriors among David’s soldiers. Once, when it was almost time to harvest [the crops], three of those 30 men went down to Adullam Cave, where David was [staying]. A group of men from the Philistia army had set up their tents in Rephaim Valley [near Jerusalem].
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
David [and his soldiers] were in the cave [because it was safe there], and [another] group of Philistia soldiers was occupying Bethlehem.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
[One day] David very much wanted [some water] to drink, and said “I wish that someone would bring me some water from the well near the gate at Bethlehem!”
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
So his three greatest warriors forced their way through the camp of Philistia soldiers and drew some water from the well, and brought it to David. But he would not drink it. Instead, he poured it out [on the ground] as an offering to Yahweh.
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
He said, “Yahweh, it would certainly not be right for me to drink this water! That would be like [RHQ] drinking the blood of these men who were willing/ready to die for me!” So he refused to drink it. That was one of the things that those three great warriors did.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
Abishai, Joab’s [younger] brother, was the leader of the 30 [greatest warriors]. [One day] he fought against 300 men and killed them all with his spear. As a result, he also became famous.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
He was the most famous of the thirty greatest warriors, and he became their leader/commander, but he was not one of the three greatest warriors.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
Jehoiada’s son Benaiah, from Kabzeel [town], also did great deeds. He killed two of the best warriors from the Moab people-group. Also, he went down into a pit on a day when snow was falling, and killed a lion there.
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
He also killed a huge soldier from Egypt who carried a spear. Benaiah [had only] his club, but he attacked the giant with it. Then he snatched the spear from the man’s hand and killed him with his own spear.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
Those are [some of] the things that Benaiah did. As a result, he became famous, like the three greatest warriors were.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
He was more honored than the other members of the group of thirty great warriors, but not as famous as the three greatest warriors. David appointed him to be the commander of his bodyguards.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
[These are the names of the great warriors]: Asahel, the brother of Joab; Elhanan, the son of Dodo, from Bethlehem;
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
Shammah and Elika, from [the] Harod [clan];
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
Helez, from Pelet [city]; Ira, the son of Ikkesh, from Tekoa [town];
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
Abiezer, from Anathoth [city]; Mebunnai [whose other name was Sibbecai], from Hushah’s [clan];
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
Zalmon [whose other name was Ilai], from Ahoh’s [clan]; Maharai, from Netophah [town];
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
Heleb, the son of Baanah, also from Netophah [town]; Ittai, the son of Ribai, from Gibeah [town] in [the land that belonged to] the tribe of Benjamin;
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Benaiah, from Pirathon [town]; Hiddai, from the valleys near Gaash [Mountain];
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
Abi-Albon, from the clan of Arabah; Azmaveth, from Bahurim [town];
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
Eliahba, from Shaalbon [town]; The sons of Jashen; Jonathan;
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
Shammah, from Harar [town/clan]; Ahiam the son of Sharar, from Harar [town/clan];
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Eliphelet, the son of Ahasbai, from Maacah [town]; Eliam, the son of Ahithophel, from Gilo [town];
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
Hezro, from Carmel [city]; Paarai, from Arba [city];
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Igal, the son of Nathan, from Zobah [city]; Bani, from the tribe of Gad;
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
Zelek, from the Ammon people-group; Naharai, the man who carried Joab’s weapons, from Beeroth [town];
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
Ira and Gareb, from Jattir [town];
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
Uriah, [Bathsheba’s husband], from the Heth people-group. Altogether, there were 37 famous soldiers, [but some of them had died and their names were not included].

< 2 Sama’ila 23 >