< 2 Sama’ila 22 >
1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
E hizo David una canción para el Señor con estas palabras, el día en que el Señor lo liberó de las manos de todos sus enemigos, y de la mano de Saúl:
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Y él dijo: El Señor es mi roca, mi fortaleza, y mi salvador;
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Dios mío, roca mía, en él pondré mi fe; mi coraza y el poder de mi salvación, mi torre alta y mi lugar seguro; Mi salvador, que me mantiene a salvo del hombre violento.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Enviaré mi clamor al Señor, quien es digno de alabanza; Así me protegeré de los que están contra mí.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Porque las olas de la muerte me rodearon, y los mares del mal me hicieron temer;
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
Los lazos del infierno me rodearon: las redes de la muerte cayeron sobre mí. (Sheol )
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
En mi angustia mi voz subió al Señor, y mi clamor a mi Dios: mi voz llegó a su oído en su santo Templo, y mi oración llegó a sus oídos.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Entonces la tierra se conmovió con un golpe violento; Las bases del cielo se movieron y temblaron, porque él estaba enojado.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
De su nariz salía humo, y de su boca salía un fuego de destrucción: encendía carbones.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Se doblaron los cielos para que descendiera; y estaba oscuro bajo sus pies.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Y atravesó el aire, sentado en una nube de tormenta, yendo rápidamente sobre las alas del viento.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
E hizo a su alrededor la oscuridad su tabernáculo, una masa de aguas, gruesas nubes de los cielos.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Un fulgor de resplandor salió de su presencia, lloviendo hielo y carbones de fuego.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
El Señor hizo truenos en los cielos, y la voz del Altísimo estaba sonando.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Y él envió sus flechas, llevándolas en todas direcciones; por sus llamas de fuego mis enemigos se turbaron.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Luego se vieron los canales profundos del mar, y se descubrieron las bases del mundo, debido a la ira del Señor, a causa del fuerte soplo del aliento de su nariz.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Me tendió la mano desde de lo alto, me tomó y me sacó de las grandes aguas.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Me liberó de mi fuerte odiador, de los que estaban contra mí, porque eran más fuertes que yo.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Ellos vinieron sobre mí en el día de mi problema, pero el Señor fue mi apoyo.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Me sacó a un lugar espacioso; Él era mi salvador porque se deleitaba en mí.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
El Señor me da la recompensa de mi justicia, porque mis manos están limpias delante de él.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Porque he guardado los caminos del Señor; No he sido apartado de mi Dios.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Porque todas sus decisiones estaban delante de mí, y no aparté de mí sus leyes.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
Y fui recto delante de él, y me guardé del pecado.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Por esto el Señor me ha dado la recompensa de mi justicia, porque mis manos están limpias en sus ojos.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Sobre el que tiene misericordia, tú tendrás misericordia; para los rectos serás recto;
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
El que es santo verá que tú eres santo; Pero para el hombre cuyo camino no es recto, serás un juez duro.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Porque tú eres el salvador de los que están en problemas; Pero tus ojos están puestos en los hombres de orgullo, para humillarlos.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Porque tú eres mi luz, oh Señor; y el Señor alumbra mi oscuridad.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Con tu ayuda, me abrí paso a través de un ejército, con la ayuda de mi Dios, he saltado sobre muros.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
En cuanto a Dios, su camino es perfecto, la palabra del Señor es purificada; Él es un escudo seguro para todos aquellos que ponen su fe en él.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Porque ¿quién es Dios sino el Señor? ¿Y quién es la roca, sino nuestro Dios?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Dios me ciñe de poder, guiándome de manera directa.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Hace mis pies ligeros como de ciervo, y me pone en lugares altos.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Él hace que mis manos sean expertas en la guerra, de modo que un arco de bronce se doble por mis brazos.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Me has dado la coraza de tu salvación, y tu misericordia me ha hecho grande.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Has ensanchado mis pasos debajo de mí, para que mis pies no se deslicen.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Voy tras mis enemigos y los alcancé; No volviendo atrás hasta que todos sean vencidos.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Les he enviado destrucción y les he dado heridas para que no puedan levantarse: están bajo mis pies.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Porque he sido armado por ti con fuerza para el combate; has abatido a los que salieron contra mí.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Has hecho que mis enemigos huyan delante de mí, y a los que me odiaban destruí.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Estaban gritando, pero no había nadie que acudiera en su ayuda: ni siquiera él Señor, les respondió.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Entonces fueron aplastados tan pequeños como el polvo de la tierra, pisoteados bajo mis pies como él lodo de las calles.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Me has liberado de las luchas de mi pueblo; Tú me has hecho cabeza de las naciones; un pueblo del cual no tenía conocimiento serán mis siervos.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Los extranjeros de otros países, se pondrán bajo mi autoridad: desde el momento en que mi nombre llegue a sus oídos, me obedecerán.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Los extranjeros se debilitarán y saldrán de sus lugares secretos temblando de miedo.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
El Señor está vivo; Alabado sea mi roca, exaltado sea él Dios de mi salvación.
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
Es Dios quien envía castigo a mis enemigos, y pone a los pueblos bajo mi gobierno.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Me libera de mis enemigos. Me levanto sobre los que me atacan: me has liberado del hombre violento.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Por eso te alabaré, oh Señor, entre las naciones, y cantaré alabanza a tu nombre.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
La gran salvación da a su rey. Y muestra su fidelidad a su pacto; tiene misericordia del rey de su elección, David, y de su descendencia para siempre.