< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
Y habló David a Jehová las palabras de este cántico, el día que Jehová le libró de la mano de todos sus enemigos, y de la mano de Saul, y dijo:
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Jehová es mi roca, y mi fortaleza, y mi librador.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Dios es mi peñasco, en él confiaré: mi escudo, y el cuerno de mi salud: mi fortaleza, y mi refugio: mi salvador, que me librarás de violencia.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
A Jehová digno de ser loado invocaré, y seré salvo de mis enemigos.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Cuando me cercaron ondas de muerte, y arroyos de iniquidad me asombraron;
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
Cuando las cuerdas del sepulcro me ciñeron, y los lazos de muerte me tomaron descuidado; (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
Cuando tuve angustia, invoqué a Jehová, y clamé a mi Dios, y él desde su templo oyó mi voz, mi clamor llegó a sus oídos.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
La tierra se removió, y tembló: los fundamentos de los cielos fueron movidos, y se estremecieron; porque él se airó.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Subió humo de sus narices, y de su boca fuego consumidor, por el cual se encendieron carbones.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Y abajó los cielos y descendió: una oscuridad debajo de sus pies.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Subió sobre el querubim, y voló: aparecióse sobre las alas del viento.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Puso tinieblas al derredor de sí como por cabañas: aguas negras, y espesas nubes.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Del resplandor de su presencia se encendieron ascuas ardientes.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
Tronó de los cielos Jehová, y el Altísimo dio su voz.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Arrojó saetas, y desbaratólos: relampagueó, y los consumió.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Entonces aparecieron los manaderos de la mar, y los fundamentos del mundo fueron descubiertos por la reprensión de Jehová, por la respiración del resuello de su nariz.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Extendió su mano de lo alto, y arrebatóme, y sacóme de las muchas aguas.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Libróme de fuertes enemigos, de los que me aborrecían, los cuales eran más fuertes que yo.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Los cuales en el día de mi calamidad me tomaron descuidado: mas Jehová fue mi bordón.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Sacóme a anchura; me libró, porque puso su voluntad en mí.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
Pagóme Jehová conforme a mi justicia: y conforme a la limpieza de mis manos me dio la paga.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Porque yo guardé los caminos de Jehová: y no me aparté impíamente de mi Dios.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Porque delante de mí tengo todas sus ordenanzas: y sus fueros, no me retiraré de ellos.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
Y fui perfecto con él, y me guardé de mi iniquidad.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Y pagóme Jehová conforme a mi justicia: y conforme a mi limpieza delante de sus ojos.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Con el bueno eres bueno, y con el valeroso perfecto, eres perfecto.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
Con el limpio eres limpio: mas con el perverso, eres perverso.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Y salvas al pueblo pobre: mas tus ojos, sobre los altivos, para abatirlos.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Porque tú eres mi lámpara, oh Jehová: Jehová da luz a mis tinieblas.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Porque en ti romperé ejércitos, y en mi Dios saltaré las murallas.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Dios, perfecto su camino: la palabra de Jehová purificada, escudo es de todos los que en él esperan.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Porque ¿qué Dios hay sino Jehová? ¿O quién es fuerte sino nuestro Dios?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Dios es el que con virtud me corrobora, y el que escombra mi camino.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
El que hace mis pies como de ciervas, y el que me asienta en mis alturas.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
El que enseña mis manos para la pelea: y el que da que yo quiebre con mis brazos el arco de acero.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Tú me diste el escudo de tu salud, y tu benignidad me ha multiplicado.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Tú ensanchaste mis pasos debajo de mí, para que no titubeasen mis rodillas.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Perseguiré mis enemigos, y quebrantarlos he, y no me volveré hasta que los acabe.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Consumirlos he, y herirlos he; que no se levantarán. Y caerán debajo de mis pies.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Ceñísteme de fortaleza para la batalla, y postraste debajo de mí los que contra mí se levantaron.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Tú me diste la cerviz de mis enemigos, de mis aborrecedores, y que yo los talase.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Miraron, y no hubo quien los librase; a Jehová, mas no les respondió.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Yo los quebrantaré como a polvo de la tierra: como a lodo de las plazas los desmenuzaré, y los disiparé.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Tú me libraste de contiendas de pueblos: tú me guardaste para que fuese cabeza de gentes: pueblos que no conocía, me sirvieron.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Los extraños titubeaban a mí; en oyendo me obedecían.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Los extraños se desleían, y temblaban en sus encerramientos.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
Viva Jehová, y sea bendita mi roca: sea ensalzado el Dios, que es la roca de mi salvamento.
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
El Dios, que me ha dado venganzas, y sujeta los pueblos debajo de mí,
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Que me saca de entre mis enemigos: tú me sacaste en alto de entre los que se levantaron contra mí: librásteme del varón de iniquidades.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Por tanto yo te confesaré en las gentes, oh Jehová, y cantaré a tu nombre.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
El que engrandece las saludes de su rey: y el que hace misericordia a su ungido David, y a su simiente para siempre.

< 2 Sama’ila 22 >