< 2 Sama’ila 22 >
1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
David je Gospodu spregovoril besede te pesmi na dan, ko ga je Gospod osvobodil iz roke vseh njegovih sovražnikov in iz Savlove roke.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Rekel je: » Gospod je moja skala in moja trdnjava in moj osvoboditelj;
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Bog moje skale; vanj bom zaupal. On je moj ščit in rog rešitve moje duše, moj visoki stolp in moje zatočišče, moj rešitelj; ti me rešuješ pred nasiljem.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Klical bom h Gospodu, ki je vreden, da je hvaljen. Tako bom rešen pred svojimi sovražniki.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Ko so me obdali valovi smrti, so me preplašile poplave brezbožnih ljudi;
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
bridkosti pekla so me obkrožile, zanke smrti so me ovirale; (Sheol )
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
v svoji stiski sem klical h Gospodu in jokal k svojemu Bogu. Iz svojega svetišča je slišal moj glas in moj jok je vstopil v njegova ušesa.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Potem se je zemlja stresla in vztrepetala, temelji neba so se premaknili in stresli, ker je bil ogorčen.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Iz njegovih nosnic se je dvignil dim in ogenj iz njegovih ust je požiral. Z njim so bili vžgani ogorki.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Upognil je tudi nebo in prišel dol in tema je bila pod njegovimi stopali.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Jahal je na kerubu in letel. Viden je bil na perutih vetra.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Vsenaokrog sebe je naredil paviljone teme, temne vode in goste oblake neba.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Od bleščave pred njim so bili vžgani ognjeni ogorki.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
Gospod je zagrmel iz nebes in Najvišji je izustil svoj glas.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Odposlal je puščice in jih razkropil; bliskanje in jih porazil.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Prikazale so se morske struge, temelji zemeljskega [kroga] so bili odkriti ob Gospodovem karanju, ob puhu sape iz njegovih nosnic.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Poslal je od zgoraj, vzel me je, potegnil me je iz mnogih vodá,
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
osvobodil me je pred mojim močnim sovražnikom in pred tistimi, ki so me sovražili, kajti zame so bili premočni.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Ovirali so me na dan moje katastrofe, toda Gospod je bil moja opora.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Prav tako me je privedel na velik kraj. Osvobodil me je, ker se je razveseljeval v meni.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
Gospod me je nagradil glede na mojo pravičnost. Poplačal mi je glede na čistost mojih rok.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Kajti držal sem se Gospodovih poti in se nisem zlobno oddvojil od svojega Boga.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Kajti vse njegove sodbe so bile pred menoj, in glede njegovih zakonov, se nisem ločil od njih.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
Pred njim sem bil tudi iskren in se zadržal pred svojo krivičnostjo.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Zatorej mi je Gospod poplačal glede na mojo pravičnost; glede na mojo čistost v njegovem pogledu.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Z usmiljenim se boš pokazal usmiljenega in s poštenim človekom se boš pokazal poštenega.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
S čistim se boš pokazal čistega in s kljubovalnim se boš pokazal neokusnega.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Stiskano ljudstvo boš rešil, toda tvoje oči so na ošabnih, da jih lahko privedeš dol.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Kajti ti si moja svetilka, oh Gospod in Gospod bo razsvetlil mojo temo.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Kajti s teboj sem tekel skozi krdelo, s svojim Bogom sem preskočil zid.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Glede Boga, njegova pot je popolna; Gospodova beseda je preizkušena. On je ščit vsem tistim, ki zaupajo vanj.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Kajti kdo je Bog, razen Gospoda? In kdo je skala, razen našega Boga?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Bog je moja sila in moč in mojo pot dela popolno.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Moje noge dela podobne nogam košut in me postavlja na moje visoke kraje.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Moje roke uči bojevanja, tako, da je jeklen lok zlomljen z mojimi lakti.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Dal si mi tudi ščit tvoje rešitve duše in tvoja blagost me je naredila velikega.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Povečal si moje korake pod menoj, tako, da moja stopala niso zdrsnila.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Zasledoval sem svoje sovražnike in jih uničil in se nisem ponovno obrnil, dokler jih nisem použil.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Použil sem jih in jih ranil, da niso mogli vstati. Da, padli so pod mojimi stopali.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Kajti opasal si me z močjo za boj. Tiste, ki se vzdigujejo zoper mene, si podjarmil pod menoj.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Dal si mi tudi vratove mojih sovražnikov, da lahko uničim tiste, ki me sovražijo.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Pogledali so, toda nikogar ni bilo, da reši; celó h Gospodu, toda ni jim odgovoril.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Potem sem jih zdrobil v zemeljski prah, pohodil sem jih kakor ulično blato in jih raztresel naokoli.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Osvobodil si me tudi pred prepiri mojega ljudstva, ohranil si me, da bi bil poglavar poganom. Ljudstvo, ki ga nisem poznal, mi bo služilo.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Tujci se mi bodo podredili; takoj ko slišijo, mi bodo poslušni.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Tujci bodo bledeli in prestrašeni bodo iz svojih zaprtih krajev.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
Gospod živi in blagoslovljena bodi moja skala in povišan bodi Bog skale rešitve moje duše.
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
To je Bog, ki me maščuje in ki ljudstvo prinaša podme
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
in ki me pelje naprej pred mojimi sovražniki. Prav tako si me dvignil na visoko, nad tiste, ki so vstali zoper mene. Osvobodil si me pred nasilnežem.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Zato se ti bom zahvaljeval, oh Gospod, med pogani in prepeval bom hvalnice tvojemu imenu.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
On je stolp rešitve duš za svojega kralja in izkazuje usmiljenje svojemu maziljencu Davidu in njegovemu semenu na vékomaj.«