< 2 Sama’ila 22 >
1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
UDavida wahlabelela uThixo amazwi alelihubo lapho uThixo wamsindisa esandleni sezitha zakhe zonke lasesandleni sikaSawuli.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Wathi: “UThixo ulidwala lami, inqaba yami lomsindisi wami;
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
uNkulunkulu wami ulidwala lami, lapho engiphephela khona, isihlangu sami lophondo lokusindiswa kwami. Uyinqaba yami, isiphephelo sami lomsindisi wami uyangisindisa ebantwini abalodlakela.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Ngakhuleka kuThixo ofanele ukudunyiswa, njalo ngikhululwe ezitheni zami.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Amagagasi okufa angikhulela; lezikhukhula zokubhubhisa zangikhulela.
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
Izibopho zengcwaba zangithandela; imijibila yokufa yangijamela. (Sheol )
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
Ekukhathazekeni kwami ngakhuleka kuThixo; ngakhala kuNkulunkulu wami. Esethempelini lakhe walizwa ilizwi lami; ukukhala kwami kwafika ezindlebeni zakhe.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Umhlaba wagedezela wazamazama, izisekelo zamazulu zanyikinyeka; zagedezela ngoba wayethukuthele.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Intuthu yalanquka emakhaleni akhe; umlilo ohangulayo waphuma emlonyeni wakhe, amalahle avuthayo alavuka ephuma kuwo.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Waqhekeza amazulu wehlela phansi; amayezi amnyama ayengaphansi kwezinyawo zakhe.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Wagada amakherubhi waphapha; wantweza phezu kwamaphiko omoya.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Wenza umnyama isigubuzelo esimhanqileyo, amayezi ezulu amnyama asemkhathini.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Phakathi kokukhazimula kobukhona bakhe, izikhatha zombane zalavuza khona.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
UThixo wakhwaza esezulwini; ilizwi loPhezukonke lanqenqetha.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Waciba imitshoko wazihlakaza izitha, ngezikhatha zombane waziqothula.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Izigodi zolwandle zambulwa lezisekelo zomhlaba zavezwa obala ekukhuzeni kukaThixo, ngomfutho wokuphefumula kwamakhala akhe.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Welula isandla sakho usezulwini wangibamba wangihlenga enzikini yamanzi.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Wangihlenga esitheni sami esilamandla, ezitheni zami ezazingigabhela ngamandla.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Zangijamela mhla ngisebunzimeni, kodwa uThixo waba yinsika yami.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Wangikhupha wangibeka endaweni ebanzi; wangihlenga ngoba wayethokoza ngami.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
UThixo ungenzele okulingene ukulunga kwami; wangivuza ngokufanele ukuhlanzeka kwezandla zami.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Ngoba ngizigcinile izindlela zikaThixo; angenzanga okubi ngokufulathela uNkulunkulu wami.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Yonke imithetho yakhe iphambi kwami; angizifulathelanga izimiso zakhe.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
Ngibe ngilokhu ngimsulwa phambi kwakhe njalo ngisixwayile isono.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
UThixo ungivuze ngokufanele ukulunga kwami; ngokufanele ukuhlanzeka kwami phambi kwakhe.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Kwabathembekileyo lawe uthembekile, kwabamsulwa lawe umsulwa,
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
kwabahlanzekileyo uziveza uhlanzekile, kodwa kwabangaqondanga uziveza ukhaliphile.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Uyabasindisa abathobekileyo; kodwa amehlo akho akhangele abazigqajayo ukuba ubehlisele phansi.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Uyisibane sami, Oh Thixo, uThixo uguqula ubumnyama bami bube yikukhanya.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Ngosizo lwakho ngingaphuma ngimelane lebutho lempi, ngoNkulunkulu wami ngingawukhwela umduli.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Izindlela zikaNkulunkulu uqobo lwakhe ziphelele; ilizwi likaThixo kalilasici. Ulihawu labo bonke abaphephela kuye.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Ngoba ngubani uNkulunkulu ngaphandle kukaThixo? Njalo ngubani oliDwala ngaphandle kukaNkulunkulu wethu na?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
NguNkulunkulu ongihlomisa amandla enze indlela yami iphelele.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Wenza inyawo zami zibe njengezempala; ungenza ngime ezingqongweni.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Ufundisa izandla zami ukulwa impi, izingalo zami zingaligobisa idandili lethusi.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Uyanginika isihlangu sakho sokunqoba; uyazehlisela phansi ukuze ungenze ngibe mkhulu.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Uqhelisa indlela enginyathela kuyo, ukuze inqagala zami zingapheci.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Ngaxotshana lezitha zami ngaziqothula; kangibuyanga ngingakazibhubhisi zonke.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Ngaziqothula okupheleleyo, njalo zazingeke zisavuka; zawela ngaphansi kwezinyawo zami.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Wangihlomisa ngamandla okulwa impi; wenza abaxabana lami bakhothama ezinyaweni zami.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Wenza izitha zami zafulathela zabaleka, njalo ngazibhubhisa izitha zami.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Bakhala becela uncedo, kodwa wayengekho owayengabahlenga kuThixo, kodwa kaphendulanga.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Ngabatshaya bacholeka njengothuli lomhlabathi; ngabagxoba ngabanyathela njengodaka ezindleleni.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Ungikhulule ekuhlaselweni yilababantu; ungigcine ngiyinhloko yezizwe. Abantu engangingabazi sebebuswa yimi,
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
abezizweni bayatshotshobala phambi kwami; bathi bengizwa nje ngendaba, bangilalele.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Bonke badelile; beza bethuthumela bevela ezinqabeni zabo.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
UThixo uyaphila! Alidunyiswe iDwala lami! Kaphakanyiswe uNkulunkulu wami, iDwala, uMsindisi wami!
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
UnguNkulunkulu ongiphindiselelayo, obeka izizwe ngaphansi kwami,
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
ongikhululayo ezitheni zami. Wena wangiphakamisela ngaphezu kwezitha zami; wangihlenga ebantwini bodlakela.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Ngakho ngizakudumisa, Oh Thixo, phakathi kwezizwe; ngizahlabelela indumiso yebizo lakho.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
Unika inkosi yakhe ukunqoba okukhulu; ubonakalisa umusa wakhe ongapheliyo kogcotshiweyo wakhe, kuDavida lenzalo yakhe kuze kube phakade.”