< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
locutus est autem David Domino verba carminis huius in die qua liberavit eum Dominus de manu omnium inimicorum suorum et de manu Saul
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
et ait Dominus petra mea et robur meum et salvator meus
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Deus meus fortis meus sperabo in eum scutum meum et cornu salutis meae elevator meus et refugium meum salvator meus de iniquitate liberabis me
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
laudabilem invocabo Dominum et ab inimicis meis salvus ero
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
quia circumdederunt me contritiones mortis torrentes Belial terruerunt me
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
funes inferi circumdederunt me praevenerunt me laquei mortis (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
in tribulatione mea invocabo Dominum et ad Deum meum clamabo et exaudiet de templo suo vocem meam et clamor meus veniet ad aures eius
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
commota est et contremuit terra fundamenta montium concussa sunt et conquassata quoniam iratus est
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
ascendit fumus de naribus eius et ignis de ore eius voravit carbones incensi sunt ab eo
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
et inclinavit caelos et descendit et caligo sub pedibus eius
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
et ascendit super cherubin et volavit et lapsus est super pinnas venti
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
posuit tenebras in circuitu suo latibulum cribrans aquas de nubibus caelorum
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
prae fulgore in conspectu eius succensi sunt carbones ignis
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
tonabit de caelis Dominus et Excelsus dabit vocem suam
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
misit sagittas et dissipavit eos fulgur et consumpsit eos
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
et apparuerunt effusiones maris et revelata sunt fundamenta orbis ab increpatione Domini ab inspiratione spiritus furoris eius
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
misit de excelso et adsumpsit me extraxit me de aquis multis
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
liberavit me ab inimico meo potentissimo ab his qui oderant me quoniam robustiores me erant
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
praevenit me in die adflictionis meae et factus est Dominus firmamentum meum
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
et eduxit me in latitudinem liberavit me quia placuit ei
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
retribuet mihi Dominus secundum iustitiam meam et secundum munditiam manuum mearum reddet mihi
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
quia custodivi vias Domini et non egi impie a Deo meo
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
omnia enim iudicia eius in conspectu meo et praecepta eius non amovi a me
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
et ero perfectus cum eo et custodiam me ab iniquitate mea
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
et restituet Dominus mihi secundum iustitiam meam et secundum munditiam manuum mearum in conspectu oculorum suorum
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
cum sancto sanctus eris et cum robusto perfectus
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
cum electo electus eris et cum perverso perverteris
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
et populum pauperem salvum facies oculisque tuis excelsos humiliabis
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
quia tu lucerna mea Domine et Domine inluminabis tenebras meas
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
in te enim curram accinctus in Deo meo transiliam murum
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Deus inmaculata via eius eloquium Domini igne examinatum scutum est omnium sperantium in se
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
quis est deus praeter Dominum et quis fortis praeter Deum nostrum
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Deus qui accingit me fortitudine et conplanavit perfectam viam meam
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
coaequans pedes meos cervis et super excelsa mea statuens me
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
docens manus meas ad proelium et conponens quasi arcum aereum brachia mea
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
dedisti mihi clypeum salutis tuae et mansuetudo mea multiplicavit me
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
dilatabis gressus meos subtus me et non deficient tali mei
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
persequar inimicos meos et conteram et non revertar donec consumam eos
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
consumam eos et confringam ut non consurgant cadent sub pedibus meis
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
accinxisti me fortitudine ad proelium incurvabis resistentes mihi sub me
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
inimicos meos dedisti mihi dorsum odientes me et disperdam eos
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
clamabunt et non erit qui salvet ad Dominum et non exaudiet eos
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
delebo eos ut pulverem terrae quasi lutum platearum comminuam eos atque conpingam
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
salvabis me a contradictionibus populi mei custodies in caput gentium populus quem ignoro serviet mihi
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
filii alieni resistent mihi auditu auris oboedient mihi
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
filii alieni defluxerunt et contrahentur in angustiis suis
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
vivit Dominus et benedictus Deus meus et exaltabitur Deus fortis salutis meae
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
Deus qui das vindictas mihi et deicis populos sub me
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
qui educis me ab inimicis meis et a resistentibus mihi elevas me a viro iniquo liberabis me
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
propterea confitebor tibi Domine in gentibus et nomini tuo cantabo
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
magnificanti salutes regis sui et facienti misericordiam christo suo David et semini eius in sempiternum

< 2 Sama’ila 22 >