< 2 Sama’ila 22 >
1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
David adressa à l’Éternel les paroles de ce cantique, lorsque l’Éternel l’eut délivré de la main de tous ses ennemis et de la main de Saül.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Il dit: L’Éternel est mon rocher, ma forteresse, mon libérateur.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Dieu est mon rocher, où je trouve un abri, Mon bouclier et la force qui me sauve, Ma haute retraite et mon refuge. O mon Sauveur! Tu me garantis de la violence.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Je m’écrie: Loué soit l’Éternel! Et je suis délivré de mes ennemis.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Car les flots de la mort m’avaient environné, Les torrents de la destruction m’avaient épouvanté;
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
Les liens du sépulcre m’avaient entouré, Les filets de la mort m’avaient surpris. (Sheol )
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
Dans ma détresse, j’ai invoqué l’Éternel, J’ai invoqué mon Dieu; De son palais, il a entendu ma voix, Et mon cri est parvenu à ses oreilles.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
La terre fut ébranlée et trembla, Les fondements des cieux frémirent, Et ils furent ébranlés, parce qu’il était irrité.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Il s’élevait de la fumée dans ses narines, Et un feu dévorant sortait de sa bouche: Il en jaillissait des charbons embrasés.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Il abaissa les cieux, et il descendit: Il y avait une épaisse nuée sous ses pieds.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Il était monté sur un chérubin, et il volait, Il paraissait sur les ailes du vent.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Il faisait des ténèbres une tente autour de lui, Il était enveloppé d’amas d’eaux et de sombres nuages.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
De la splendeur qui le précédait S’élançaient des charbons de feu.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
L’Éternel tonna des cieux, Le Très-Haut fit retentir sa voix;
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Il lança des flèches et dispersa mes ennemis, La foudre, et les mit en déroute.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Le lit de la mer apparut, Les fondements du monde furent découverts, Par la menace de l’Éternel, Par le bruit du souffle de ses narines.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Il étendit sa main d’en haut, il me saisit, Il me retira des grandes eaux;
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Il me délivra de mon adversaire puissant, De mes ennemis qui étaient plus forts que moi.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Ils m’avaient surpris au jour de ma détresse, Mais l’Éternel fut mon appui.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Il m’a mis au large, Il m’a sauvé, parce qu’il m’aime.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
L’Éternel m’a traité selon ma droiture, Il m’a rendu selon la pureté de mes mains;
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Car j’ai observé les voies de l’Éternel, Et je n’ai point été coupable envers mon Dieu.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Toutes ses ordonnances ont été devant moi, Et je ne me suis point écarté de ses lois.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
J’ai été sans reproche envers lui, Et je me suis tenu en garde contre mon iniquité.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Aussi l’Éternel m’a rendu selon ma droiture, Selon ma pureté devant ses yeux.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Avec celui qui est bon tu te montres bon, Avec l’homme droit tu agis selon la droiture,
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
Avec celui qui est pur tu te montres pur, Et avec le pervers tu agis selon sa perversité.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Tu sauves le peuple qui s’humilie, Et de ton regard, tu abaisses les orgueilleux.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Oui, tu es ma lumière, ô Éternel! L’Éternel éclaire mes ténèbres.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Avec toi je me précipite sur une troupe en armes, Avec mon Dieu je franchis une muraille.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Les voies de Dieu sont parfaites, La parole de l’Éternel est éprouvée; Il est un bouclier pour tous ceux qui se confient en lui.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Car qui est Dieu, si ce n’est l’Éternel? Et qui est un rocher, si ce n’est notre Dieu?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
C’est Dieu qui est ma puissante forteresse, Et qui me conduit dans la voie droite.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Il rend mes pieds semblables à ceux des biches, Et il me place sur mes lieux élevés.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Il exerce mes mains au combat, Et mes bras tendent l’arc d’airain.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Tu me donnes le bouclier de ton salut, Et je deviens grand par ta bonté.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Tu élargis le chemin sous mes pas, Et mes pieds ne chancellent point.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Je poursuis mes ennemis, et je les détruis; Je ne reviens pas avant de les avoir anéantis.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Je les anéantis, je les brise, et ils ne se relèvent plus; Ils tombent sous mes pieds.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Tu me ceins de force pour le combat, Tu fais plier sous moi mes adversaires.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Tu fais tourner le dos à mes ennemis devant moi, Et j’extermine ceux qui me haïssent.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Ils regardent autour d’eux, et personne pour les sauver! Ils crient à l’Éternel, et il ne leur répond pas!
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Je les broie comme la poussière de la terre, Je les écrase, je les foule, comme la boue des rues.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Tu me délivres des dissensions de mon peuple; Tu me conserves pour chef des nations; Un peuple que je ne connaissais pas m’est asservi.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Les fils de l’étranger me flattent, Ils m’obéissent au premier ordre.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Les fils de l’étranger sont en défaillance, Ils tremblent hors de leurs forteresses.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
Vive l’Éternel, et béni soit mon rocher! Que Dieu, le rocher de mon salut, soit exalté,
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
Le Dieu qui est mon vengeur, Qui m’assujettit les peuples,
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Et qui me fait échapper à mes ennemis! Tu m’élèves au-dessus de mes adversaires, Tu me délivres de l’homme violent.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
C’est pourquoi je te louerai parmi les nations, ô Éternel! Et je chanterai à la gloire de ton nom.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
Il accorde de grandes délivrances à son roi, Et il fait miséricorde à son oint, A David, et à sa postérité, pour toujours.