< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
And David spoke to the Lord the words of this verse, in the day that the Lord freed him from the hand of all his enemies and from the hand of Saul.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
And he said: “The Lord is my rock, and my strength, and my Savior.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
I will hope in him. God is my strong one, my shield, and the horn of my salvation. He lifts me up, and he is my refreshment. You, O my Savior, will free me from iniquity.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
I will call upon the Lord, who is praiseworthy; and I will be saved from my enemies.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
For the pangs of death have encircled me. The torrents of Belial have terrified me.
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
The ropes of Hell have encompassed me. The snares of death have intercepted me. (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
In my tribulation, I will call upon the Lord, and I will cry out to my God. And he will heed my voice from his temple, and my outcry will reach his ears.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
The earth was shaken, and it quaked. The foundations of the mountains were struck together and violently shaken, because he was angry with them.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Smoke ascends from his nostrils, and fire from his mouth will devour; coals have been kindled by it.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
He bent down the heavens, and it descended; and a fog was beneath his feet.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
And he climbed upon the cherubim, and he flew; and he slid upon the wings of the wind.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
He set darkness as a hiding place around himself, with waters sifted from the clouds of the heavens.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
By means of the brightness of his glance, coals of fire were kindled.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
The Lord will thunder from heaven; and the Most High will utter his voice.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
He shot arrows, and he scattered them; lightning, and he consumed them.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
And the overflow of the sea appeared, and the foundations of the globe were revealed, at the rebuke of the Lord, at the exhale of the breath of his fury.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
He sent from on high, and he took me up. And he drew me out of many waters.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
He freed me from my most powerful enemy and from those who had hated me. For they were too strong for me.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
He went before me in the day of my affliction, and the Lord became my firmament.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
And he led me out to a wide-open place. He freed me, because I was pleasing to him.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
The Lord will reward me according to my justice. And he will repay me according to the cleanness of my hands.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
For I have kept to the ways of the Lord, and I have not acted impiously before my God.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
For all his judgments are in my sight. And I have not removed his precepts from me.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
And I shall be perfect with him. And I shall guard myself from my own iniquity.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
And the Lord will recompense me according to my justice, and according to the cleanness of my hands in the sight of his eyes.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
With the holy one, you will be holy, and with the strong one, you will be perfect.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
With the elect one, you will be elect, and with the perverse one, you will be perverse.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
And you will bring to salvation the poor people, and you will humble the exalted with your eyes.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
For you are my lamp, O Lord. And you, O Lord, will illuminate my darkness.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
For in you, I will run girded. In my God, I will leap over the wall.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
God, his way is immaculate; the eloquence of the Lord is an exacting fire. He is the shield of all who hope in him.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Who is God except the Lord? And who is strong except our God?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
God, he has girded me with fortitude, and he has made my way perfect:
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
making my feet like the feet of the stag, and stationing me upon my exalted places,
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
teaching my hands to do battle, and making my arms like a bow of brass.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
You have given me the shield of your salvation. And your mildness has multiplied me.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
You will enlarge my steps under me, and my ankles will not fail.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
I will pursue my enemies, and crush them. And I will not turn back, until I consume them.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
I will consume them and break them apart, so that they cannot rise up; they will fall under my feet.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
You have girded me with strength for the battle. Those who resisted me, you have bent down under me.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
You have caused my enemies to turn their back to me; they have hatred for me, and I shall destroy them.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
They will cry out, and there will be no one to save; to the Lord, and he will not heed them.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
I will wipe them away like the dust of the earth. I will break them apart and crush them, like the mud of the streets.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
You will save me from the contradictions of my people. You will preserve me to be the head of the Gentiles; a people I do not know shall serve me.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
The sons of foreigners, who will resist me, at the hearing of the ear they will be obedient to me.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
The foreigners flowed away, but they will be drawn together in their anguishes.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
The Lord lives, and my God is blessed. And the strong God of my salvation shall be exalted.
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
God gives me vindication, and he casts down the peoples under me.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
He leads me away from my enemies, and he lifts me up from those who resist me. You will free me from the iniquitous man.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Because of this, I will confess to you, O Lord, among the Gentiles, and I will sing to your name:
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
magnifying the salvation of his king, and showing mercy to David, his Christ, and to his offspring forever.”

< 2 Sama’ila 22 >