< 2 Sama’ila 22 >
1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
David upravi Jahvi riječi ove pjesme u dan kad ga je Jahve izbavio iz ruku svih njegovih neprijatelja i iz ruke Šaulove.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Pjevao je: “Jahve, hridino moja, utvrdo moja, spase moj;
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Bože moj, pećino moja kojoj se utječem, štite moj, spasenje moje, tvrđavo moja! Ti me izbavljaš od nasilja.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Zazvat ću Jahvu hvale predostojna i od dušmana bit ću izbavljen.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Valovi smrti okružiše mene, prestraviše me bujice pogubne,
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
Užad Podzemlja sputiše me, smrtonosne zamke padoše na me: (Sheol )
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
u nevolji zazvah Jahvu i Bogu svome zavapih. Iz svog Doma zov mi začu, i vapaj moj mu do ušiju doprije.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
I zemlja se potrese i uzdrhta, uzdrmaše se temelji nebesa, pokrenuše se, jer On gnjevom planu.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Iz nosnica mu dim se diže, iz usta mu oganj liznu, ugljevlje živo od njega plamsa.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
On nagnu nebesa i siđe, pod nogama oblaci mu mračni.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Na keruba stade i poletje; na krilima vjetra zaplovi.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Ogrnu se mrakom kao koprenom, prekri se tamnim vodama i oblacima tmastim,
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
od bljeska pred licem njegovim užga se ugljevlje plameno.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
Jahve s neba zagrmje, Svevišnjega glas se ori.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Odape strijele i dušmane rasu, izbaci munje i na zemlju ih obori.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Morska dna se pokazaše, i temelji svijeta postaše goli od strašne prijetnje Jahvine, od olujna daha gnjeva njegova.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
On pruži s neba ruku i mene prihvati, iz silnih voda on me izbavi.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Od protivnika moćnog mene oslobodi, od dušmana mojih jačih od mene.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Navališe na me u dan zlosretni, ali me Jahve zaštiti,
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
na polje prostrano izvede me, spasi me jer sam mu mio.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
Po pravednosti mojoj Jahve mi uzvrati, po čistoći ruku mojih on me nagradi,
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
jer čuvah putove Jahvine, od Boga se svoga ne udaljih.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Odredbe njegove sve su mi pred očima, zapovijedi njegove nisam odbacio,
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
do srži odan njemu sam bio, čuvam se grijeha svakoga.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Jahve mi po pravdi mojoj vrati, čistoću ruku mojih vidje.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
S prijateljem ti si prijatelj, poštenu poštenjem uzvraćaš.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
S čovjekom čistim ti si čist, a lukavca izigravaš,
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
jer narodu poniženu spasenje donosiš a ponižavaš oči ohole.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Jahve, ti moju svjetiljku užižeš, Bože, tminu moju obasjavaš:
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
s tobom udaram na čete dušmanske, s Bogom svojim preskačem zidine.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Savršeni su puti Gospodnji, i riječ je Jahvina ognjem kušana. on je štit svima, samo on, koji se k njemu utječu.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Jer tko je Bog osim Jahve? Tko li je hridina osim Boga našega?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Taj Bog me snagom opasuje, stere mi put besprijekoran.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Noge mi dade brze ko u košute i postavi me na visine sigurne,
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
ruke mi za borbu uvježba i mišice da luk mjedeni napinju.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Daješ mi štit svoj koji spasava, tvoja me brižljivost uzvisi.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Pouzdanje daješ mom koraku, i noge mi više ne posrću.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Pognah svoje dušmane i dostigoh, i ne vratih se dok ih ne uništih.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Obaram ih, ne mogu se dići, padaju, pod nogama mi leže.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Ti me opasa snagom za borbu, a protivnike moje meni podloži.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Ti dušmane moje u bijeg natjera, i rasprših one koji su me mrzili.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Vapiju u pomoć, nikog da pomogne, vapiju Jahvi - ne odaziva se.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Smrvih ih kao prah na vjetru, zgazih ih ko blato na putu.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Ti me §izbavÄi od bune u mom narodu, postavi me glavarom pogana, puk koji ne poznavah služi mi.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Svaki moj šapat pokorno on sluša. Sinovi tuđinci meni laskaju,
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
sinovi tuđinski gube srčanost izlaze dršćuć iz svojih utvrda.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
Živio Jahve! Blagoslovljena hridina moja! Neka se uzvisi Bog, spasenje moje!
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
Bog koji mi daje osvetu i narode meni pokorava.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Od dušmana me mojih izbavljaš i nad protivnike me moje izdižeš, ti mene od čovjeka silnika spasavaš.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Zato te slavim, Jahve, među pucima i psalam pjevam tvome Imenu:
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
umnožio si pobjede kralju svojemu, pomazaniku svome milost si iskazao, Davidu i potomstvu njegovu navijeke.”