< 2 Sama’ila 21 >

1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
I Davids tid var det engang en hungersnød som varte i tre år efter hverandre. Da søkte David Herrens åsyn, og Herren svarte: Det er fordi det hviler blodskyld på Saul og hans hus, siden han drepte gibeonittene.
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
Kongen lot da gibeonittene kalle og talte med dem. Gibeonittene hørte ikke til Israels barn, men var av de amoritter som var blitt tilbake i landet, og Israels barn hadde svoret dem en ed, men Saul søkte å slå dem ihjel i sin nidkjærhet for Israels og Judas barn.
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
David sa til gibeonittene: Hvad skal jeg gjøre for eder, og hvormed skal jeg gjøre soning, så I velsigner Herrens arv?
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
Gibeonittene svarte: Vi krever ikke sølv eller gull hos Saul og hans hus, og vi har ikke rett til å drepe nogen mann i Israel. Han sa: Hvad I krever, vil jeg gjøre for eder.
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
Og de sa til kongen: Den mann som ødela oss, og som hadde i sinne å utrydde oss, så det ikke skulde finnes nogen av oss igjen innen hele Israels landemerker -
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
la oss av hans sønner få syv menn, så vil vi henge dem op for Herren i Gibea, hvor Saul, Herrens utvalgte, hørte hjemme. Kongen svarte: Jeg skal gi eder dem.
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
Kongen sparte Mefiboset, sønn av Jonatan, Sauls sønn, for den eds skyld som de - David og Jonatan, Sauls sønn - hadde svoret hverandre ved Herren.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
Men de to sønner som Rispa, Ajas datter, hadde fått med Saul, Armoni og Mefiboset, og de fem sønner som Mikal, Sauls datter, hadde fått med Adriel, sønn av meholatitten Barsillai, dem tok kongen
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
og overgav dem til gibeonittene, og de hengte dem op på fjellet for Herrens åsyn; de omkom alle syv på en gang. Det var i de første dager av høsten, i begynnelsen av bygghøsten, de blev drept.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
Men Rispa, Ajas datter, tok sin sørgedrakt og bredte den ut på klippen fra høstens begynnelse inntil det strømmet vann ned på dem fra himmelen; og hun lot ikke himmelens fugler få slå ned på dem om dagen eller markens ville dyr om natten.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
Da David fikk vite hvad Rispa, Ajas datter, Sauls medhustru, hadde gjort,
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
tok han avsted og hentet Sauls og hans sønn Jonatans ben fra mennene i Jabes i Gilead, som hemmelig hadde tatt dem bort fra torvet i Betsan; der hadde filistrene hengt dem op den dag de slo Saul på Gilboa.
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
Og da han hadde ført Sauls og hans sønn Jonatans ben op derfra, samlet de også benene av dem som var hengt,
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
og de begravde Sauls og hans sønn Jonatans ben i Benjamins land, i Sela, i hans far Kis' grav. De gjorde alt det kongen hadde befalt. Og derefter hørte Gud landets bønn.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
Atter kom det til krig mellem filistrene og Israel; og David drog ned med sine menn, og de stred med filistrene. David blev trett,
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
og Jisbo-Benob, som hørte til Rafas barn - han hadde en lanse som veide tre hundre sekel kobber, og han var omgjordet med et nytt sverd - han tenkte på å slå David ihjel.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
Men Abisai, Serujas sønn, kom ham til hjelp og slo filisteren og drepte ham. Da svor Davids menn og sa til ham: Du skal ikke mere dra ut med oss i striden, forat du ikke skal utslukke Israels lys.
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
Siden blev det atter strid med filistrene; det var ved Gob; da slo husatitten Sibbekai Saf, som hørte til Rafas barn.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
Ennu en gang blev det strid med filistrene ved Gob, og betlehemitten Elhanan, sønn av Ja'are-Orgim, slo gittitten Goliat, som hadde et spyd hvis skaft var som en veverstang.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
Så kom det atter til strid ved Gat. Der var en høivoksen mann som hadde seks fingrer på hver hånd og seks tær på hver fot - i alt fireogtyve fingrer og tær; han var og en efterkommer av Rafa.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
Han hånte Israel; men Jonatan, sønn av Davids bror Simea, hugg ham ned.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
Disse fire var efterkommere av Rafa i Gat, og de falt for Davids og hans menns hånd.

< 2 Sama’ila 21 >