< 2 Sama’ila 21 >
1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
Or il y eut du temps de David une famine qui dura trois ans de suite. Et David rechercha la face de l'Eternel; et l'Eternel lui répondit: C'est à cause de Saül et de sa maison sanguinaire; parce qu'il a fait mourir les Gabaonites.
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
Alors le Roi appela les Gabaonites pour leur parler. Or les Gabaonites n'étaient point des enfants d'Israël, mais un reste des Amorrhéens; et les enfants d'Israël leur avaient juré [de les laisser vivre]; mais Saül par un zèle qu'il avait pour les enfants d'Israël et de Juda, avait cherché de les faire mourir.
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
Et David dit aux Gabaonites: Que vous ferai-je, et par quel moyen vous apaiserai-je; afin que vous bénissiez l'héritage de l'Eternel?
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
Et les Gabaonites lui répondirent: Nous n'avons à faire ni de l'or ni de l'argent de Saül et de sa maison, ni qu'on fasse mourir personne en Israël. Et [le Roi leur] dit: Que demandez-vous donc que je fasse pour vous?
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
Et ils répondirent au Roi: Quant à cet homme qui nous a détruits, et qui a machiné contre nous, en sorte que nous ayons été exterminés, sans pouvoir subsister dans aucune des contrées d'Israël;
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
Qu'on nous livre sept hommes de ses fils, et nous les mettrons en croix devant l'Eternel, au coteau de Saül, l'Elu de l'Eternel. Et le Roi leur dit: Je vous les livrerai.
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
Or le Roi épargna Méphiboseth fils de Jonathan, fils de Saül, à cause du serment que David et Jonathan fils de Saül avaient fait entr'eux [au nom] de l'Eternel.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
Mais le Roi prit les deux fils de Ritspa fille d'Aja, qu'elle avait enfantés à Saül, savoir Armoni et Méphiboseth, et les cinq fils de Mical fille de Saül, qu'elle avait nourris à Hadriel fils de Barzillaï Méholathite.
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
Et il les livra entre les mains des Gabaonites, qui les mirent en croix sur la montagne devant l'Eternel; et ces sept-là furent tués ensemble, et on les fit mourir aux premiers jours de la moisson, [savoir] au commencement de la moisson des orges.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
Alors Ritspa fille d'Aja prit un sac, et le tendit pour elle au dessus d'un rocher, depuis le commencement de la moisson jusqu'à ce qu'il tombât de l'eau du ciel sur eux; et elle ne souffrait point qu'aucun oiseau des cieux se posât sur eux de jour, ni aucune bête des champs la nuit.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
Et on rapporta à David ce que Ritspa, fille d'Aja, concubine de Saül, avait fait.
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
Et David s'en alla, et prit les os de Saül, et les os de Jonathan son fils, que les habitants de Jabés de Galaad avaient enlevés de la place de Beth-san, où les Philistins les avaient pendus, le jour qu'ils avaient tué Saül en Guilboah.
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
Il emporta donc de là les os de Saül, et les os de Jonathan son fils. On recueillit aussi les os de ceux qui avaient été mis en croix;
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
Et on les ensevelit avec les os de Saül et de Jonathan son fils au pays de Benjamin, à Tsélah, dans le sépulcre de Kis père de Saül; et on fit tout ce que le Roi avait commandé. Et après cela, Dieu fut apaisé envers le pays.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
Or il y avait eu aussi une autre guerre des Philistins contre les Israélites; et David y était allé, et ses serviteurs avec lui, et ils avaient tellement combattu contre les Philistins, que David défaillait.
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
Et Jisbi-benob, qui était des enfants de Rapha, et qui avait une lance dont le fer pesait trois cents sicles d'airain, et qui était armé d'une nouvelle manière, avait résolu de frapper David.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
Mais Abisaï fils de Tséruja vint à son secours, et frappa le Philistin, et le tua. Alors les gens de David jurèrent, en disant: Tu ne sortiras plus avec nous en bataille, de peur que tu n'éteignes la Lampe d'Israël.
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
Après cela il y eut une autre guerre à Gob contre les Philistins, où Sibbécaï le Husathite frappa Saph, qui était des enfants de Rapha.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
Il y eut encore une autre guerre à Gob contre les Philistins, en laquelle Elhanan, fils de Jaharé Oreguim Bethléhémite frappa [le frère] de Goliath Guittien, qui avait une hallebarde dont la hampe [était] comme l'ensuble d'un tisserand.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
Il y eut encore une autre guerre à Gath, où il se trouva un homme d'une taille extraordinaire, qui avait six doigts à chaque main, et six orteils à chaque pied, en tout vingt et quatre, lequel était aussi de la race de Rapha.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
Cet homme défia Israël; mais Jonathan fils de Simha, frère de David, le tua.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
Ces quatre-là naquirent à Gath, de la race de Rapha, et moururent par les mains de David, ou par les mains de ses serviteurs.