< 2 Sama’ila 21 >

1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
Et du temps de David, il y eut une famine qui dura trois années consécutives. David questionna le Seigneur, et le Seigneur dit: Sur Saül et sur sa maison pèse une iniquité qui demande encore de son sang, parce qu'il a mis à mort les Gabaonites.
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
Le roi David appela les Gabaonites, et il s'entretint avec eux. Or, les Gabaonites ne sont point fils d'Israël, mais un débris des Amorrhéens, et les fils d'Israël leur avaient prêté serment; malgré cela, Saül entreprit de les exterminer, dans son zèle pour les fils d'Israël et de Juda.
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
David dit donc aux Gabaonites: Que puis-je faire pour vous? comment pourrai-je vous apaiser afin que vous bénissiez l'héritage du Seigneur?
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
Et les Gabaonites répondirent: Entre nous et entre Saül et sa famille, il n'est question ni d'argent, ni d'or, et nul en Israël ne doit, à cause de nous, mourir. Et David reprit: Que voulez-vous dire? Parlez, je le ferai pour vous.
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
Et ils dirent au roi: L'homme qui a tourné contre nous ses forces, qui nous a traqués, qui a conçu le vain projet de nous exterminer, nous voulons l'effacer de sorte qu'il ne reste rien de lui, sur tout le territoire d'Israël.
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
Livre-nous sept de ses fils, afin qu'en Gabaon, ville de Saül, nous les exposions au soleil pour le Seigneur; sept fils de Saül, choisis pour le Seigneur. Et le roi dit: Je vous les livrerai.
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
Le roi épargna Miphiboseth, fils de Jonathan, fils de Saül, à cause du serment du Seigneur que s'étaient mutuellement prêté Jonathan et David.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
Mais il prit les deux fils de Respha, fille d'Ais, qu'elle avait eus de Saül: Hermoni et Miphiboseth, et les cinq fils de Michol, fille de Saül, qu'elle avait eus d'Esdriel, fils de Berzelli, le Moülathite.
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
Et il les remit aux Gabaonites, qui les exposèrent au soleil, sur la montagne, devant le Seigneur, et tous les sept succombèrent ensemble. Ils moururent dans les premiers jours de la moisson, comme on commençait à couper les orges.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
Et Respha, fille d'Aïa, prit un cilice, et, au commencement de la moisson des orges, elle se plaça près de la roche; elle y demeura jusqu'à ce que l'eau du ciel tombât sur les morts, et elle ne laissa pas les oiseaux du ciel se poser sur eux, pendant le jour, ni les bêtes fauves des champs les atteindre, pendant la nuit.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
On alla dire à David ce que faisait Respha, fille d'Aïa, concubine de Saül; puis, on détacha les cadavres; et Dan, fils de Joa, de la race des géants, les prit.
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
Après cela, David partit, et il reprit les ossements de Saül et ceux de Jonathan, aux hommes de Jabès-Galaad qui les avaient dérobés dans les rues de Bethsam, où les Philistins les avaient cloués, le jour de leur victoire sur Saül en Gelboé.
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
Et il rapporta de cette ville les ossements de Saül et ceux de Jonathan, et il recueillit les ossements des sept exposés au soleil.
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
Et l'on ensevelit tous ces ossements, en Benjamin, sur les flancs de la montagne, dans le sépulcre de Cis, père de Saül; on exécuta tout ce que David avait prescrit, et après cela Dieu exauça les vœux de la terre.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
Ensuite, la guerre s'alluma encore entre les Philistins et Israël. David se mit en campagne avec ses serviteurs; dans une bataille contre les Philistins, lui-même sortit des rangs, et de l'autre côté,
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
Jesbi, de la race des géants. Celui-ci portait une javeline dont la pointe pesait trois cents sicles d'airain; à sa ceinture pendait une massue, et il pensait tuer David.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
Mais Abessa vint au secours du roi; il frappa le Philistin et il le tua. Alors, les hommes de David jurèrent et dirent: Tu ne viendras plus à la guerre avec nous, de peur que tu n'éteignes la lampe d'Israël.
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
Après cela, il y eut encore un combat près de Geth avec les Philistins. Alors, Sebocha, d'Astaroth, tua Seph, de la race des géants.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
Puis, il y eut une bataille à Rhom avec les Philistins, et Eléanan, fils d'Ariorgim de Bethléem, tua Goliath le Géthéen, qui portait une javeline dont le bois ressemblait au mât d'un tisserand.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
Il y eut encore un combat à Geth. Et il y avait un homme de grande taille, ayant six doigts à chaque main et six doigts à chaque pied, en tout vingt-quatre doigts. Et il était aussi de la race des géants.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
Et il défiait Israël; il fut tué par Jonathan, fils de Sémeï, frère de David.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
Tous les quatre étaient issus des géants, et ils étaient nés à Geth dans la famille de Rhapha, et ils tombèrent sous les coups de David ou de ses serviteurs.

< 2 Sama’ila 21 >