< 2 Sama’ila 21 >

1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
Du temps de David, il y eut une famine pendant trois ans, année après année, et David chercha la face de Yahvé. Yahvé dit: « C'est à cause de Saül et de sa maison sanglante, parce qu'il a fait mourir les Gibéonites. »
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
Le roi appela les Gabaonites et leur dit (les Gabaonites n'étaient pas d'entre les enfants d'Israël, mais d'entre les restes des Amoréens; les enfants d'Israël leur avaient fait un serment, et Saül cherchait à les tuer dans son zèle pour les enfants d'Israël et de Juda);
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
et David dit aux Gabaonites: « Que dois-je faire pour vous? Et avec quoi dois-je faire l'expiation, afin que vous bénissiez l'héritage de Yahvé? ».
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
Les Gabaonites lui dirent: « Il n'est question ni d'argent ni d'or entre nous et Saül ou sa maison, et il ne nous appartient pas de faire mourir quelqu'un en Israël. » Il a dit: « Je ferai pour toi tout ce que tu dis. »
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
Ils dirent au roi: « L'homme qui nous a consumés et qui a comploté contre nous pour que nous soyons détruits et que nous ne puissions rester dans aucune des frontières d'Israël,
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
qu'on nous livre sept hommes de ses fils, et nous les pendrons à Yahvé à Guibea de Saül, l'élu de Yahvé. » Le roi a dit: « Je vais les donner. »
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
Mais le roi épargna Mephiboscheth, fils de Jonathan, fils de Saül, à cause du serment de l'Éternel qui était entre eux, entre David et Jonathan, fils de Saül.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
Mais le roi prit les deux fils de Ritspa, fille d'Aja, qu'elle avait enfantés à Saül, Armoni et Mephibosheth, et les cinq fils de Merab, fille de Saül, qu'elle avait enfantés à Adriel, fils de Barzillai, le Méholathien.
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
Il les livra entre les mains des Gabaonites, qui les pendirent sur la montagne devant Yahvé, et tous les sept tombèrent ensemble. Ils furent mis à mort les jours de la moisson, les premiers jours, au début de la récolte de l'orge.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
Ritspa, fille d'Aja, prit un sac et s'en étendit sur le rocher, depuis le début de la moisson jusqu'à ce que l'eau tombe du ciel sur eux. Elle ne permit ni aux oiseaux du ciel de s'y reposer le jour, ni aux animaux des champs la nuit.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
On raconta à David ce qu'avait fait Ritspa, fille d'Aja, concubine de Saül.
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
David alla prendre les ossements de Saül et les ossements de Jonathan, son fils, chez les hommes de Jabesh Galaad, qui les avaient volés dans la rue de Beth Shan, où les Philistins les avaient pendus le jour où les Philistins tuèrent Saül à Gilboa;
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
et il fit monter de là les ossements de Saül et les ossements de Jonathan, son fils. Ils recueillirent aussi les ossements de ceux qui avaient été pendus.
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
On enterra les ossements de Saül et de Jonathan, son fils, dans le pays de Benjamin, à Zéla, dans le tombeau de Kis, son père, et on exécuta tout ce que le roi avait ordonné. Après cela, Dieu a répondu à la prière pour le pays.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
Les Philistins firent de nouveau la guerre à Israël; David descendit, et ses serviteurs avec lui, et combattit les Philistins. David s'affaiblit;
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
et Ishbibenob, qui était d'entre les fils du géant, et dont la lance pesait trois cents sicles d'airain, armé d'une épée neuve, pensait tuer David.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
Mais Abishaï, fils de Tseruja, lui vint en aide, frappa le Philistin et le tua. Les hommes de David lui jurèrent alors: « Ne sors plus avec nous pour combattre, afin que tu n'éteignes pas la lampe d'Israël. »
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
Après cela, il y eut de nouveau une guerre avec les Philistins à Gob. Et Sibbecaï, le Hushathite, tua Saph, qui était d'entre les fils du géant.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
Il y eut encore une guerre avec les Philistins à Gob, et Elhanan, fils de Jaaré-Oregim, le Bethléhémite, tua le frère de Goliath, le Gittien, dont le bâton de la lance était comme une poutre de tisserand.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
Il y eut encore une guerre à Gath, où se trouvait un homme de grande taille, qui avait six doigts à chaque main et six orteils à chaque pied, au nombre de vingt-quatre.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
Lorsqu'il défia Israël, Jonathan, fils de Schimeï, frère de David, le tua.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
Ces quatre-là étaient nés du géant à Gath, et ils tombèrent par la main de David et par la main de ses serviteurs.

< 2 Sama’ila 21 >