< 2 Sama’ila 21 >

1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
And there was a famine in the days of David three years, year after year; and David besought the presence of the Lord. And the Lord said, On account of Saul, and on account of the house of blood, is this; because he hath slain the Gib'onites.
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
And the king called for the Gib'onites, and said unto them: [now the Gib'onites are not of the children of Israel, but of the remnant of the Emorites; and the children of Israel had sworn unto them; but Saul had sought to slay them in his zeal for the children of Israel in Judah: ]
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
Wherefore David said unto the Gib'onites, What shall I do for you? and wherewith shall I make the atonement, that ye may bless the inheritance of the Lord?
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
And the Gib'onites said unto him, We have no concern of silver or gold with Saul and with his house: nor do we wish to kill any man in Israel. And he said, What ye say, will I do for you.
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
And they said to the king, The man that consumed us, and that devised against us that we should be destroyed, so that we should have no footing in all the boundaries of Israel.
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
Let there be delivered unto us seven men of his sons, and we will hang them up unto the Lord in Gib'ah of Saul, the chosen of the Lord. And the king said, I will give them.
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
But the king had pity on Mephibosheth, the son of Jonathan the son of Saul, because of the Lord's oath that was between them, between David and Jonathan the son of Saul.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
And the king took the two sons of Rizpah the daughter of Ayah, whom she had born unto Saul, Armoni and Mephibosheth; and the five sons of Michal the daughter of Saul, whom she had brought up for 'Adriel the son of Barzillai the Mecholathite:
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
And he delivered them into the hand of the Gib'onites, and they hanged them on the mount before the Lord; and they fell, these seven, together; and they were put to death in the first days of harvest, in the beginning of the barley-harvest.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
And Rizpah the daughter of Ayah took sackcloth, and spread out it for herself upon the rock, from the beginning of the harvest until water dropped down upon them out of heaven, and she suffered neither the birds of heaven to rest on them by day, nor the beasts of the field by night.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
And it was told to David what Rizpah the daughter of Ayah, the concubine of Saul, had done.
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
And David then went and took the bones of Saul and the bones of Jonathan his son from the men of Yabeshgil'ad, who had stolen them from the market-place of Bethshan, where the Philistines had hanged them up, at the time the Philistines had smitten Saul at Gilboa':
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
And he brought up from there the bones of Saul and the bones of Jonathan his son; and they gathered up the bones of those that had been hanged.
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
And they buried the bones of Saul and Jonathan his son in the country of Benjamin at Zela', in the sepulchre of Kish his father: and they performed all that the king had commanded. And after that God was entreated for the land.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
And the Philistines had again a war with Israel; and David went down, and his servants with him, and fought against the Philistines: and David became fatigued.
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
And Yishbi at Nob, who was of the children of the Raphah, the weight of whose spear was three hundred shekels of copper, he being girded with a new armor, thought to slay David.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
But Abishai the son of Zeruyah succored him, and smote the Philistine, and killed him. Then swore the men of David unto him, saying, Thou shalt go out no more with us to battle, that thou mayest not quench the lamp of Israel.
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
And it came to pass after this, that there was again a battle at Gob, with the Philistines: then smote Sibbechai the Chushathite Saph, who was of the children of the Raphah.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
And there was again a battle at Gob with the Philistines, when Elchanan the son of Ya'are-oregim, the Bethlechemite, slew Goliath the Gittite, the staff of whose spear was like a weaver's beam.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
And there was again a battle in Gath, where was a man of [great] stature, that had on every hand six fingers, and on every foot six toes, [in all] four and twenty in number; and he also was born to the Raphah.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
And he defied Israel; but Jonathan the son of Shim'ah, the brother of David, slew him.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
These four were born to the Raphah in Gath; and they fell by the hand of David, and by the hand of his servants.

< 2 Sama’ila 21 >