< 2 Sama’ila 21 >

1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
And there was a famine in the days of David for three years successively: and David consulted the oracle of the Lord. And the Lord said: It is for Saul, and his bloody house, because he slew the Gabaonites.
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
Then the king, calling for the Gabaonites, said to them: (Now the Gabaonites were not of the children of Israel, but the remains of the Amorrhites: I and the children of Israel had sworn to them, and Saul sought to slay them out of zeal, as it were for the children of Israel and Juda: )
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
David therefore said to the Gabaonites: What shall I do for you? and what shall be the atonement for you, that you may bless the inheritance of the Lord?
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
And the Gabaonites said to him: We have no contest about silver and gold, but against Saul and against his house: neither do we desire that any man be slain of Israel. And the king said to them: What will you then that I should do for you?
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
And they said to the king: The man that crushed us and oppressed us unjustly, we must destroy in such manner that there be not so much as one left of his stock in all the coasts of Israel.
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
Let seven men of his children be delivered unto us, that we may crucify them to the Lord in Gabaa of Saul, once the chosen of the Lord. And the king said: I will give them.
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
And the king spared Miphiboseth the son of Jonathan the son of Saul, because of the oath of the Lord, that had been between David and Jonathan the son of Saul.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
So the king took the two sons of Respha the daughter of Aia, whom she bore to Saul, Armoni, and Miphiboseth: and the five sons of Michol the daughter of Saul, whom she bore to Hadriel the son of Berzellai, that was of Molathi:
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
And gave them into the hands of the Gabaonites: and they crucified them on a hill before the Lord: and these seven died together in the first days of the harvest, when the barley began to be reaped.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
And Respha the daughter of Aia took haircloth, and spread it under her upon the rock from the beginning of the harvest, till water dropped upon them out of heaven: and suffered neither the birds to tear them by day, nor the beasts by night.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
And it was told David, what Respha the daughter of Aia, the concubine of Saul, had done.
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
And David went, and took the bones of Saul, and the bones of Jonathan his son from the men of Jabes Galaad, who had stolen them from the street of Bethsan, where the Philistines had hanged them when they had slain Saul in Gelboe.
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
And he brought from thence the bones of Saul, and the bones of Jonathan his son, and they gathered up the bones of them that were crucified,
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
And they buried them with the bones of Saul, and of Jonathan his son in the land of Benjamin, in the side, in the sepulchre of Cis his father: and they did all that the king had commanded, and God shewed mercy again to the land after these things.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
And the Philistines made war again against Israel, and David went down, and his servants with him, and fought against the Philistines. And David growing faint,
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
Jesbibenob, who was of the race of Arapha, the iron of whose spear weighed three hundred ounces, being girded with a new sword, attempted to kill David.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
And Abisai the son of Sarvia rescued him, and striking the Philistine killed him. Then David’s men swore unto him, saying: Thou shalt go no more out with us to battle, lest thou put out the lamp of Israel.
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
There was also a second battle in Gob against the Philistines: then Sobochai of Husathi slew Saph of the race of Arapha of the family of the giants.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
And there was a third battle in Gob against the Philistines, in which Adeodatus the son of the Forrest an embroiderer of Bethlehem slew Goliath the Gethite, the shaft of whose spear was like a weaver’s beam.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
A fourth battle was in Geth. where there was a man of great stature, that had six fingers on each hand, and six toes on each foot, four and twenty in all, and he was of the race of Arapha.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
And he reproached Israel: and Jonathan the son of Samae the brother of David slew him.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
These four were born of Arapha in Geth, and they fell by the hand of David, and of his servants.

< 2 Sama’ila 21 >