< 2 Sama’ila 20 >

1 Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
Ahora, por casualidad, estaba presente un hombre perverso llamado Seba, el hijo de Bicri, un Benjamita, y él, sonando el cuerno, dijo: No tenemos parte en David, ni ningún interés en el Hijo de Isaí, que cada uno vaya a su tienda, oh Israel.
2 Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
Entonces todos los hombres de Israel, apartándose de David, fueron tras Seba, el hijo de Bicri, pero los hombres de Judá fueron fieles a su rey, y lo acompañaron desde el Jordán hasta Jerusalén.
3 Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
Y vino David a su casa en Jerusalén; y el rey llevó a las diez concubinas a quienes había dejado el cuidado de la casa, las encerró bajo custodia y les dio las necesidades de la vida, pero no volvió a tener relaciones con ellas. Así que fueron encerradas hasta el día de su muerte, viviendo como viudas.
4 Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
Entonces el rey dijo a Amasa: Reúne a todos los hombres de Judá, y tu también preséntate en tres días aquí.
5 Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
Entonces Amasa fue a reunir a todos los hombres de Judá, pero él tomó más tiempo del que David le había dado.
6 Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
Entonces David dijo a Abisai: Seba, el hijo de Bicri, nos hará más daño que Absalón; así que toma algunos de los sirvientes de tu señor y ve tras él, antes de que se ponga a salvo en las ciudades amuralladas y se escape ante nuestros ojos.
7 Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
Y fueron después Abisai, Joab y los cereteos, los peleteos y todos los combatientes; Salieron de Jerusalén para alcanzar a Seba, el hijo de Bicri.
8 Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
Cuando estaban en la gran piedra que está en Gabaón, Amasa se encontró cara a cara con ellos. Ahora Joab llevaba puesto su traje de guerra, y alrededor de él un cinturón de la que colgaba su espada en su cubierta; y mientras caminaba, se le salió, cayendo al suelo.
9 Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
Y Joab dijo a Amasa: ¿Está bien, hermano mío? Y con su mano derecha lo tomó por el pelo de su barbilla para darle un beso.
10 Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
Pero Amasa no vio peligro por la espada que estaba ahora en la mano izquierda de Joab, y Joab se la pasó por el estómago y todos sus intestinos se derramaron en el suelo, y no le dio otro golpe. Entonces Joab y su hermano Abisai siguieron a Seba, el hijo de Bicri.
11 Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
Y uno de los jóvenes de Joab, tomando su lugar al lado de Amasa, dijo: Quienquiera que sea para Joab y para David, ¡que vaya tras Joab!
12 Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
Y Amasa estaba tendido en un charco de sangre en medio de la carretera. Y cuando el hombre vio que toda la gente se estaba deteniendo, sacó a Amasa de la carretera y lo puso en un campo, con un paño sobre él, cuando vio que todos los que iban se detuvieron parados junto a él.
13 Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
Cuando lo sacaron del camino, todas las personas siguieron a Joab en busca de Seba, el hijo de Bicri.
14 Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
Y Seba pasó por todas las tribus de Israel a Abel de Bet-maaca; Y todos los descendientes de Bicri se juntaron y entraron tras él.
15 Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
Y Joab y sus hombres lo encerraron en Abel de Bet-maaca, y levantaron un rampa de tierra contra la ciudad: y todos los hombres de Joab hicieron todo lo posible por derribar el muro.
16 Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
Entonces una mujer sabia se levantó en la pared y, gritando desde el pueblo, dijo: Oye, oye; Di ahora a Joab: acércate, para que pueda hablar contigo.
17 Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
Y él se acercó, y la mujer dijo: ¿Eres tú Joab? Y él respondió: Yo soy. Entonces ella dijo: Escucha las palabras de tu sierva. Y él dijo: Estoy escuchando.
18 Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
Entonces ella dijo: En los viejos tiempos, hubo un dicho: Pongan la pregunta en Abel y en Dan, diciendo: ¿Ha llegado a su fin lo que los hombres de buena fe en Israel han ordenado?
19 Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
Tu propósito es la destrucción de una ciudad madre en Israel: ¿por qué pondrías fin a la herencia del Señor?
20 Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
Y respondiendo Joab, le dijo: Lejos, lejos de mí, sea causa de muerte o destrucción;
21 Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
No es así, pero un hombre de la región montañosa de Efraín, Seba, hijo de Bicri, por su nombre, ha tomado las armas contra el rey, contra David: abandone a este hombre solamente, y me iré del pueblo. Y la mujer le dijo a Joab: Su cabeza caerá sobre la pared hacia ti.
22 Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
Entonces la mujer en su sabiduría había hablado con todo el pueblo. Y le cortaron la cabeza a Seba y la enviaron a Joab. Y él hizo sonar el cuerno de retirada, y los envió a todos lejos de la ciudad, cada hombre a su tienda. Y Joab volvió a Jerusalén al rey.
23 Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
Y Joab estaba sobre todo el ejército; y Benaía, el hijo de Joiada, estaba al mando de los cereteos y los peleteos;
24 Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
Y Adoram era el supervisor del trabajo forzado; y Josafat, el hijo de Ahilud, fue el registrador;
25 Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
Y Seva era el escriba, y Sadoc y Abiatar eran sacerdotes;
26 Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.
Y además, Ira él Jaireo era sacerdote de David.

< 2 Sama’ila 20 >