< 2 Sama’ila 20 >

1 Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
Ngalesosikhathi kwenzakala ukuthi umxabanisi owayethiwa nguShebha indodana kaBhikhiri umBhenjamini abekhona. Wakhalisa icilongo waklabalala esithi, “Kasilasabelo kuDavida, kasilangxenye endodaneni kaJese! Umuntu wonke ethenteni lakhe, Oh Israyeli!”
2 Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
Ngakho bonke abantu bako-Israyeli bahlubuka kuDavida balandela uShebha indodana kaBhikhiri. Kodwa abantu bakoJuda babambelela enkosini yabo umango wonke kusukela eJodani kusiya eJerusalema.
3 Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
UDavida esebuyele esigodlweni sakhe eJerusalema, wathatha abafazi bakhe beceleni abalitshumi ayebatshiye begcine isigodlo wababeka endlini elindwayo. Wabanika ababekuswela, kodwa kembathanga labo. Babehlala bevalelwe kuze kube lusuku lokufa kwabo, baphila njengabafelokazi.
4 Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
Inkosi yasisithi ku-Amasa, “Biza abantu bakoJuda beze kimi phakathi kwensuku ezintathu, lawe ube lapha wena ngokwakho.”
5 Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
Kodwa u-Amasa eseyebiza uJuda, wathatha isikhathi eside kulaleso inkosi eyayimisele sona.
6 Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
UDavida wasesithi ku-Abhishayi, “Khathesi uShebha indodana kaBhikhiri uzasenzela umonakalo odlula owenziwa ngu-Abhisalomu. Thatha abantu benkosi yakho umlandele, hlezi athole amadolobho avikelweyo aphunyuke kithi.”
7 Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
Ngakho abantu bakaJowabi lamaKherethi lamaPhelethi kanye lamaqhawe wonke alamandla baphuma belawulwa ngu-Abhishayi. Bahamba besuka eJerusalema belandela uShebha indodana kaBhikhiri.
8 Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
Kwathi besesedwaleni elikhulu eGibhiyoni, u-Amasa wayabahlangabeza. UJowabi wayegqoke ibhatshi lakhe lempi, phezu kwalo, ekhalweni lwakhe, kubophe ibhanti lilomhedla esikhwameni sawo. Esahamba esiya phambili, umhedla wawela ngaphandle kwesikhwama sawo.
9 Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
UJowabi wasesithi ku-Amasa, “Unjani, mfowethu?” UJowabi wasebamba u-Amasa ngendevu ngesandla sakhe sokudla wasemanga.
10 Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
U-Amasa kawunanzelelanga umhedla owawuphethwe nguJowabi, uJowabi wasemgwaza esiswini sakhe, amathumbu akhe ahutshukela phandle emhlabathini. Lanxa engasagwazwanga futhi, u-Amasa wafa. Emva kwalokho uJowabi lomfowabo u-Abhishayi baxotshana loShebha indodana kaBhikhiri.
11 Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
Omunye wabantu bakaJowabi wema phansi kuka-Amasa wathi, “Lowo othanda uJowabi, lalowo ongokaDavida, kalandele uJowabi!”
12 Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
U-Amasa walala ezibhixeka egazini lakhe phakathi komgwaqo, umuntu lowo wabona ukuthi amabutho wonke afika ame khonapho. Kwathi esenanzelele ukuthi umuntu wonke owafika ku-Amasa wema, wamhudula emsusa emgwaqweni wamusa egangeni, waphosela isembatho phezu kwakhe.
13 Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
Emva kokuba u-Amasa esesusiwe emgwaqweni, abantu bonke bedlula loJowabi ukuyaxotshana loShebha indodana kaBhikhiri.
14 Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
UShebha wadabula phakathi kwazo zonke izizwana zako-Israyeli kusiya e-Abheli-Bhethi-Mahakha laphakathi kwesabelo sonke samaBikiri, aqoqanayo amlandela.
15 Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
Wonke amabutho ayeloJowabi afika amvimbezela uShebha e-Abheli-Bhethi-Mahakha. Bakha idundulu lokuvimbezela elalifika edolobheni njalo laleyame izinqaba zangaphandle. Besagqula umduli ukuba bawudilize,
16 Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
owesifazane ohlakaniphileyo wamemeza esedolobheni wathi, “Lalelani! Lalelani! Tshelani uJowabi eze lapha ukuze ngikhulume laye.”
17 Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
Wahamba esiya kuye, wasembuza esithi, “UnguJowabi na?” Yena waphendula wathi, “Nginguye.” Wasesithi, “Lalela okuzatshiwo yincekukazi yakho.” Wathi, “Ngilalele.”
18 Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
Owesifazane waqhubeka wathi, “Kudala babejwayele ukuthi, ‘Funani impendulo e-Abheli-Bhethi-Mahakha,’ lokho kwakuyiqeda indaba.
19 Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
Thina singabathuleyo labathembekileyo ko-Israyeli. Wena uzama ukudiliza idolobho elingunina ko-Israyeli. Kungani ufuna ukuginya ilifa likaThixo na?”
20 Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
UJowabi waphendula wathi, “Akusikho lokho! Akusikho lokho ukuginya loba ukudiliza!
21 Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
Akunjalo. Umuntu othiwa nguShebha indodana kaBhikhiri, owaselizweni lezintaba lako-Efrayimi, uphakamisele inkosi isandla sakhe emelana layo, emelana loDavida. Mletheni umuntu lowo, ngisuke edolobheni.” Owesifazane wathi kuJowabi “Ikhanda lakhe lizaphoswa kuwe lisuka emdulini.”
22 Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
Emva kwalokho owesifazane lowo waya ebantwini bonke leseluleko sakhe esikhaliphileyo, baquma ikhanda likaShebha indodana kaBhikhiri baliphosela kuJowabi. Ngakho wakhalisa icilongo, abantu bakhe bachitheka besuka edolobheni, lowo lalowo ebuyela emzini wakhe. UJowabi wabuyela enkosini eJerusalema.
23 Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
UJowabi wayephethe lonke ibutho lako-Israyeli; uBhenaya indodana kaJehoyada ephethe amaKherethi lamaPhelethi;
24 Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
u-Adoniramu wayephethe izibhalwa; uJehoshafathi indodana ka-Ahiludi wayengumbhali;
25 Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
uSheva engumabhalane; uZadokhi lo-Abhiyathari bengabaphristi;
26 Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.
u-Ira umJayiri engumphristi kaDavida.

< 2 Sama’ila 20 >