< 2 Sama’ila 20 >
1 Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
Il arriva aussi que là était un homme de Bélial, du nom de Séba, fils de Bochri, homme de Jémini, et il sonna de la trompette, et dit: Nous n’avons point de part avec David, ni d’héritage avec le fils d’Isaï; retourne en tes tabernacles, ô Israël.
2 Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
Et tout Israël se sépara de David, et suivit Séba, fils de Bochri; mais les hommes de Juda restèrent près de leur roi, depuis le Jourdain jusqu’à Jérusalem.
3 Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
Et lorsque le roi fut venu en sa maison à Jérusalem, il prit les dix femmes qu’il avait laissées pour garder la maison, les donna en garde, leur fournissant les aliments; et il ne s’approcha plus d’elles: mais elles étaient enfermées jusqu’au jour de leur mort, vivant en veuves.
4 Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
Or, le roi dit à Amasa: Appelle près de moi tous les hommes de Juda pour le troisième jour, et toi, sois présent.
5 Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
Amasa donc s’en alla pour appeler Juda, et il tarda au-delà de l’ordre que lui avait donné le roi.
6 Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
Or David dit à Abisaï: Maintenant Séba, fils de Bochri, nous affligera plus qu’Absalom: prends donc les serviteurs de ton seigneur, et poursuis-le, de peur qu’il ne trouve des villes fortifiées, et qu’il ne nous échappe.
7 Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
Les hommes de Joab sortirent donc avec lui, les Céréthiens aussi et les Phélétiens; et tous les hommes vigoureux sortirent de Jérusalem pour poursuivre Séba, fils de Bochri.
8 Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
Et lorsqu’ils furent près de la grande pierre qui est à Gabaon, Amasa, venant, les rencontra. Or, Joab était vêtu d’une tunique étroite, selon la mesure de son habit, et par-dessus ceint d’un glaive pendant à ses côtés dans son fourreau, et fait de manière qu’il pouvait par un léger mouvement sortir et frapper.
9 Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
C’est pourquoi Joab dit à Amasa: Salut, mon frère. Et de sa main droite, il prit le menton d’Amasa, comme pour le baiser.
10 Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
Or Amasa ne prit point garde au glaive qu’avait Joab, qui le frappa dans le côté, et répandit ses entrailles sur la terre; et il ne le frappa point d’un second coup, et Amasa mourut. Ensuite Joab et Abisaï son frère poursuivirent Séba, fils de Bochri.
11 Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
Cependant quelques hommes des compagnons de Joab, s’étant arrêtés près du cadavre d’Amasa, dirent: Voilà celui qui a voulu être de la suite de David à la place de Joab.
12 Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
Et Amasa, couvert de sang, gisait au milieu de la voie. Mais un certain homme vit que tout le peuple s’arrêtait pour le voir; il poussa Amasa de la voie dans le champ, et le couvrit d’un vêtement, afin que les passants ne s’arrêtassent pas à cause de lui.
13 Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
Amasa donc ôté de la voie, tout homme passait, suivant Joab, pour poursuivre Séba, fils de Bochri.
14 Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
Mais celui-ci avait passé à travers toutes les tribus d’Israël, à Abéla et à Bethmaacha; et tous les hommes choisis s’étaient assemblés auprès de lui.
15 Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
C’est pourquoi Joab et les siens vinrent, et l’assiégèrent à Abéla et à Bethmaacha; et ils environnèrent la ville de fortifications, et la ville fut investie: or, toute la multitude qui était avec Joab s’efforçait de détruire les murs.
16 Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
Et une femme sage de la ville s’écria: Ecoutez, écoutez; dites à Joab: Approche-toi d’ici, et je te parlerai.
17 Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
Lorsque Joab se fut approché d’elle, elle lui dit: C’est toi qui es Joab? Et celui-ci répondit: Moi. Elle lui parla ainsi: Ecoute les paroles de ta servante. Joab répondit: J’écoute.
18 Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
Et elle de nouveau: Ce mot, dit-elle, se disait dans un ancien proverbe: Ceux qui interrogent, qu’ils interrogent à Abéla; et c’est ainsi qu’ils arrivaient au but.
19 Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
N’est-ce pas moi qui réponds la vérité en Israël, et toi, tu demandes à bouleverser une cité, et à détruire une mère en Israël? Pourquoi renverses-tu l’héritage du Seigneur?
20 Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
Et répondant, Joab dit: Loin de moi, loin de moi cela! je ne renverse, ni ne démolis.
21 Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
La chose n’est pas ainsi; mais un homme de la montagne d’Ephraïm, Séba, fils de Bochri par son surnom, a levé sa main contre le roi David: livrez-le seul, et nous nous retirerons de la ville. Et la femme dit à Joab: Voilà que sa tête te sera envoyée par-dessus le mur.
22 Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
Elle s’avança donc vers tout le peuple, et parla sagement; et ayant coupé la tête de Séba, fils de Bochri, ils la jetèrent à Joab. Et celui-ci sonna de la trompette, et ils se retirèrent de la ville, chacun en ses tabernacles; mais Joab retourna à Jérusalem près du roi.
23 Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
Joab donc fut chef de toute l’armée d’Israël, mais Banaïas, fils de Joïada, des Céréthiens et des Phéléthiens,
24 Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
Et Aduram, des tributs; et Josaphat, fils d’Ahilud, tenait les registres.
25 Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
Siva était scribe, et Sadoc et Abiathar, prêtres.
26 Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.
Mais Ira, le Jaïrite, était prêtre de David.