< 2 Sama’ila 20 >
1 Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
Or, il se trouva là un misérable du nom de Chéba, fils de Bikhri, Benjamite; il sonna du cor et proclama: "Nous n’avons aucune part à David, aucune communauté à revendiquer avec le fils de Jessé; chacun à ses tentes, ô Israël!"
2 Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
Et tout Israël abandonna le parti de David pour suivre Chéba, tandis que les hommes de Juda, depuis le Jourdain jusqu’à Jérusalem, restèrent attachés à leur roi.
3 Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
Le roi David, étant rentré dans sa demeure à Jérusalem, prit les dix concubines qu’il avait commises à la garde du palais et les mit dans un lieu de dépôt, où il pourvut à leurs besoins mais il n’approcha point d’elles, et elles restèrent séquestrées jusqu’au jour de leur mort, en état de veuvage perpétuel.
4 Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
Le roi dit à Amasa: "Rassemble-moi les hommes de Juda dans les trois jours, puis tu attendras ici."
5 Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
Amasa partit pour rassembler Juda, mais il dépassa le terme qui lui était assigné.
6 Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
Alors David dit à Abisaï: "Chéba, fils de Bikhri, va maintenant devenir plus dangereux pour nous que ne fut Absalon. Prends, toi, les serviteurs de ton maître et mets-toi à sa poursuite: il pourrait avoir trouvé des villes fortes et échapper à nos regards."
7 Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
A sa suite sortirent les gens de Joab, les Kerêthi et Pelêthi, tous les vaillants; ils partirent de Jérusalem à la poursuite de Chéba, fils de Bikhri.
8 Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
Comme ils se trouvaient près de la grande pierre qui est à Gabaon, ils virent arriver Amasa. Joab était alors ceint de son costume de guerre, par-dessus lequel était le ceinturon de l’épée, fixée près de la cuisse dans son fourreau. Elle s’échappa tandis qu’il s’avançait.
9 Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
Joab dit à Amasa: "Comment vas-tu, mon frère?" et de la main droite il saisit la barbe d’Amasa pour l’embrasser.
10 Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
Amasa ne se méfia pas de l’épée qui était dans la main de Joab; celui-ci l’en frappa dans l’aine, et les entrailles se répandirent à terre sans qu’il portât un second coup, et Amasa mourut, tandis que Joab, avec son frère Abisaï, poursuivait Chéba, fils de Bikhri.
11 Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
Quelqu’un des serviteurs de Joab resta près du corps, en disant: "Qui aime Joab et qui tient pour David, que celui-là suive Joab!"
12 Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
Cependant Amasa se roulait dans son sang au milieu du chemin; l’homme, voyant que tout le peuple s’arrêtait là, transporta Amasa de la route dans un champ et jeta un manteau sur son corps, parce qu’il avait remarqué que tous ceux qui arrivaient près de lui s’arrêtaient.
13 Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
Une fois le corps enlevé de la route, chacun passa à la suite de Joab, afin de faire la chasse à Chéba, fils de Bikhri.
14 Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
Celui-ci traversa toutes les tribus d’Israël jusqu’à Abêl dit aussi Beth-Maakha et tous les Bêrim; les autres se massèrent, le suivirent aussi de près,
15 Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
et, arrivés, l’assiégèrent dans Abêl Beth-Maakha; ils dressèrent contre la ville un remblai qui atteignit l’avant-mur, et déjà toute la troupe de Joab faisait effort contre la muraille pour la renverser,
16 Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
lorsqu’une femme avisée cria de la ville: "Ecoutez, écoutez! Dites à Joab d’approcher pour que je lui parle!"
17 Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
Et Joab s’approcha d’elle, et elle dit: "Es-tu Joab? Je le suis. Ecoute les paroles de ta servante. J’Écoute."
18 Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
Elle reprit en ces termes: "Il aurait fallu commencer par des pourparlers, c’est-à-dire interroger les habitants d’Abêl, et on eût ainsi tout terminé.
19 Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
Nous sommes parmi les plus paisibles et fidèles en Israël, et tu voudrais anéantir une ville, une métropole d’Israël! Pourquoi veux-tu supprimer l’héritage du Seigneur?
20 Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
Loin de moi, répondit Joab, loin de moi de vouloir supprimer ou détruire!
21 Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
Tel n’est point le cas. Mais un homme de la montagne d’Ephraïm Chéba, fils de Bikhri, est son nom s’est insurgé contre le roi, contre David; livrez-le, lui seul, et je me retirerai de la ville. Eh bien! dit cette femme à Joab, sa tête te sera jetée par-dessus la muraille.
22 Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
Et elle harangua tout le peuple dans sa sagesse, et on trancha la tête à Chéba, fils de Bikhri, et on la jeta à Joab; il sonna du cor et, s’éloignant de la ville, chacun regagna sa tente, tandis que Joab retournait à Jérusalem auprès du roi.
23 Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
Joab resta à la tête de l’armée d’Israël; Benaïa, fils de Joïada, commandait aux Kerêthi et Pelêthi;
24 Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
Adoram était préposé aux impôts; Josaphat, fils d’Ahiloud, archiviste;
25 Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
Scheva, secrétaire; Çadok et Ebiathar, prêtres;
26 Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.
et Ira, le Yaïri, lui aussi, était ministre de David.