< 2 Sama’ila 20 >
1 Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
Now, in that place, there happened to be an abandoned man, whose name, was Sheba son of Bichri, a man of Benjamin, —so he blew a horn, and said—We have no share in David, Nor inheritance have we in the son of Jesse, Every man to his home, O Israel!
2 Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
Then went up all the men of Israel from following David, to follow Sheba son of Bichri, —but, the men of Judah, clave unto their king, from the Jordan, even as far as Jerusalem.
3 Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
And David entered into his own house, in Jerusalem, and the king took the ten women, the concubines whom he had left to keep the house, and put them in ward, and sustained them, but, unto them, went he not in, —so they were shut up until the day of their death, in lifelong widowhood.
4 Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
Then said the king unto Amasa, Assemble me the men of Judah, within three days, —and, thou, here, take thy stand!
5 Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
So Amasa went, to assemble Judah, —but he tarried beyond the fixed time, which he had appointed him.
6 Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
Then said David unto Abishai, Now, shall Sheba son of Bichri, do us more harm than Absolom, —thou, take the servants of thy lord, and pursue him, lest he have got him into fortified cities, and so have escaped our eye.
7 Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
Then went out after him—the men of Joab, and the Cherethites and the Pelethites, and all the mighty men, —and they went out from Jerusalem, to pursue Sheba son of Bichri.
8 Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
When, they, were by the great stone which is in Gibeon, Amasa, had arrived before them. Now, Joab, was girded about with his war-coat as his upper garment, and, over it, a girdle with a sword, fastened upon his loins, in the sheath thereof, and, it, came out and fell.
9 Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
Then said Joab unto Amasa, Art thou, well, my brother? And Joab took Amasa by the beard with his right hand, to kiss him.
10 Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
Amasa not heeding the sword that was in the hand of Joab, he smote him therewith in the belly, and shed out his bowels to the ground, and [struck] him not again, and he died. So, Joab and Abishai his brother, pursued Sheba son of Bichri.
11 Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
Now, a man, stood over him, of the young men of Joab, —and said—Whosoever is well pleased with Joab, and whosoever pertaineth to David, let him follow Joab.
12 Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
But, Amasa, was wallowing in blood, in the midst of the highway, —and, when the man saw that all the people stood still, he moved Amasa, out of the highway into the field, and cast over him a garment, as soon as he saw that every man that came up to him stood still.
13 Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
When he had removed him out of the highway, every man passed on, after Joab, to pursue Sheba son of Bichri.
14 Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
And he passed on throughout all the tribes of Israel, unto Abel and unto Beth-maachah, and all the Berites, —and they were called together, and came in, yea and followed him.
15 Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
So they came, and laid siege against him, in Abel, Beth-maachah, and they cast up a mound against the city, so that it stood within a rampart, —and, all the people who were with Joab, were battering the wall to throw it down.
16 Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
Then cried a wise woman out of the city, —Hear ye! hear ye! I pray you, say unto Joab, Come near hither, and let me speak unto thee.
17 Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
So he came near unto her, and the woman said, —Art thou Joab? And he said, —I am. And she said unto him, —Hear thou the words of thy handmaid. And he said, I do hear.
18 Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
Then spake she, saying, —They, used to speak, in former times, saying, Enquire, in Abel! And, so, they ended it.
19 Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
I, am of the peaceable among the faithful in Israel, —thou, art seeking to put to death a city, and a mother in Israel, wherefore wouldst thou swallow up the inheritance of Yahweh?
20 Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
Then answered Joab and said, —Far be it! far be it from me! I will neither swallow up nor lay waste.
21 Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
Not so, is the matter! but, a man of the hill country of Ephraim, Sheba son of Bichri, his name, hath lifted up his hand against the king, even against David, give up him alone, and I will depart from the city. And the woman said unto Joab, Lo! his head, shall be cast unto thee, through the wall.
22 Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
So the woman came unto all the people in her wisdom, and they cut off the head of Sheba son of Bichri, and cast it out unto Joab. And he blew with a horn, and they dispersed themselves from the city, every man to his home; but, Joab, returned to Jerusalem unto the king.
23 Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
And, Joab, was [restored] unto all the army of Israel, —And, Benaiah, son of Jehoiada, was over the Cherethites and over the Pelethites,
24 Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
And, Adoniram, was over the tribute, —And, Jehoshaphat, son of Ahilud, was the remembrancer;
25 Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
And, Sheva, was scribe, —And, Zadok and Abiathar, were priests;
26 Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.
Moreover also, Ira the Jairite, was chief ruler unto David.