< 2 Sama’ila 2 >

1 Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
بعد از آن، داوود از خداوند سؤال کرد: «آیا به یکی از شهرهای یهودا برگردم؟» خداوند در پاسخ او فرمود: «بله.» داوود پرسید: «به کدام شهر بروم؟» خداوند جواب داد: «به حِبرون برو.»
2 Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
پس داوود با دو زن خود اخینوعم یزرعیلی و ابیجایل، بیوهٔ نابال کرملی
3 Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
و با همهٔ افرادش و خانواده‌های آنان به حبرون کوچ کرد.
4 Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
آنگاه رهبران یهودا نزد داوود آمده، او را در آنجا برای پادشاهی تدهین کردند تا بر سرزمین یهودا حکمرانی کند. داوود چون شنید که مردان یابیش جلعاد شائول را دفن کرده‌اند،
5 sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
برای ایشان چنین پیغام فرستاد: «خداوند شما را برکت دهد زیرا نسبت به پادشاه خود شائول وفاداری خود را ثابت کرده، او را دفن نمودید.
6 Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
خداوند برای این کارتان به شما پاداش بدهد. من نیز به نوبهٔ خود این خوبی شما را جبران خواهم کرد.
7 Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
حالا که شائول مرده است، قبیلهٔ یهودا مرا به عنوان پادشاه جدید خود قبول کرده‌اند. پس نترسید و شجاع باشید!»
8 Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
اما ابنیر، پسر نیر، فرماندهٔ سپاه شائول به اتفاق ایشبوشت پسر شائول از رود اردن گذشته، به محنایم فرار کرده بودند.
9 Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
در آنجا ابنیر ایشبوشت را بر جلعاد، اشیر، یزرعیل، افرایم، بنیامین و بقیهٔ اسرائیل پادشاه ساخت.
10 Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
ایشبوشت چهل ساله بود که پادشاه اسرائیل شد و دو سال سلطنت کرد. اما قبیلهٔ یهودا داوود را رهبر خود ساختند و داوود در حبرون هفت سال و شش ماه در سرزمین یهودا سلطنت کرد.
11 Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
12 Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
روزی سپاهیان ایشبوشت به فرماندهی ابنیر، پسر نیر، از محنایم به جبعون آمدند.
13 Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
سپاهیان داوود نیز به فرماندهی یوآب (پسر صرویه) به مقابلهٔ آنها برآمدند. نیروها در کنار برکهٔ جبعون در مقابل هم قرار گرفتند.
14 Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
ابنیر به یوآب گفت: «چطور است چند نفر را از دو طرف به میدان بفرستیم تا با هم بجنگند؟» یوآب موافقت نمود.
15 Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
پس از هر طرف دوازده نفر انتخاب شدند.
16 Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
هر یک از آنها با یک دست سر حریف خود را گرفته، با دست دیگر شمشیر را به پهلویش می‌زد، تا اینکه همه مردند. از آن به بعد آن مکان که در جبعون است به «میدان شمشیرها» معروف شد.
17 Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
به دنبال این کشتار، جنگ سختی بین دو طرف درگرفت و یوآب و نیروهای داوود، ابنیر و مردان اسرائیل را شکست دادند.
18 ’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
ابیشای و عسائیل، برادران یوآب نیز در این جنگ شرکت داشتند. عسائیل مثل آهو می‌دوید.
19 Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
او به تعقیب ابنیر پرداخت و لحظه‌ای از او چشم برنمی‌داشت.
20 Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
ابنیر وقتی سرش را برگرداند و به عقب نگاه کرد، دید عسائیل او را تعقیب می‌کند. او را صدا زده، گفت: «آیا تو عسائیل هستی؟» عسائیل جواب داد: «بله، خودمم.»
21 Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
ابنیر به او گفت: «برو با کسی دیگر بجنگ! سراغ یکی از جوانان برو و خلع سلاحش کن!» اما عسائیل همچنان به تعقیب ابنیر ادامه داد.
22 Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
ابنیر بار دیگر فریاد زد: «از تعقیب من دست بردار. اگر تو را بکشم دیگر نمی‌توانم به صورت برادرت یوآب نگاه کنم.»
23 Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
ولی عسائیل دست بردار نبود. پس ابنیر با سر نیزه‌اش چنان به شکم او زد که سر نیزه از پشتش درآمد. عسائیل جابه‌جا نقش بر زمین شد و جان سپرد. هر کس به مکانی که نعش او افتاده بود می‌رسید، می‌ایستاد.
24 Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
ولی یوآب و ابیشای به تعقیب ابنیر پرداختند. وقتی به تپهٔ امه نزدیک جیح که سر راه بیابان جبعون است رسیدند، آفتاب غروب کرده بود.
25 Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
سپاهیان ابنیر که از قبیلهٔ بنیامین بودند، بر فراز تپهٔ امه گرد آمدند.
26 Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
ابنیر، یوآب را صدا زده، گفت: «تا کی می‌خواهی این کشت و کشتار ادامه یابد؟ این کار عاقبت خوشی ندارد. چرا دستور نمی‌دهی افرادت از تعقیب برادران خود دست بکشند؟»
27 Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
یوآب در جواب او گفت: «به خدای زنده قسم، اگر این حرف را نمی‌زدی تا فردا صبح شما را تعقیب می‌کردیم.»
28 Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
آنگاه یوآب شیپورش را زد و مردانش از تعقیب سربازان اسرائیلی دست کشیدند.
29 Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
همان شب ابنیر و افرادش برگشته، از رود اردن عبور کردند. آنها تمام صبح روز بعد نیز در راه بودند تا سرانجام به محنایم رسیدند.
30 Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
یوآب و همراهانش نیز به خانه برگشتند. تلفات افراد داوود غیر از عسائیل فقط نوزده نفر بود.
31 Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
ولی از افراد ابنیر (که همه از قبیلهٔ بنیامین بودند) سیصد و شصت نفر کشته شده بودند.
32 Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.
یوآب و افرادش، جنازهٔ عسائیل را به بیت‌لحم برده، او را در کنار قبر پدرش به خاک سپردند. بعد، تمام شب به راه خود ادامه داده، سپیدهٔ صبح به حبرون رسیدند.

< 2 Sama’ila 2 >