< 2 Sama’ila 2 >

1 Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
Et après cela David consulta le Seigneur, disant: Est-ce que je monterai dans une des villes de Juda? Et le Seigneur lui dit: Monte. Alors David demanda: Où monterai-je? Et le Seigneur lui répondit: À Hébron.
2 Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
David donc monta, et ses deux femmes Achinoam, Jezraélite, et Abigaïl, femme de Nabal du Carmel.
3 Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
Mais David mena aussi les hommes qui étaient avec lui, chacun avec sa maison; et ils demeurèrent dans les villes d’Hébron.
4 Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
Alors vinrent les hommes de Juda, et ils oignirent là David, afin qu’il régnât sur la maison de Juda. Et on annonça à David que les hommes de Jabès-Galaad avaient enseveli Saül.
5 sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
David donc envoya des messagers aux hommes de Jabès-Galaad, et leur dit: Bénis soyez du Seigneur, vous qui avez fait cette miséricorde à votre seigneur Saül, et l’avez enseveli!
6 Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
Et maintenant le Seigneur vous rendra miséricorde et fidélité; mais moi aussi je vous rendrai grâces de ce que vous avez fait cette action.
7 Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
Que vos mains se fortifient, et soyez des fils de courage; car, quoique votre seigneur Saül soit mort, néanmoins la maison de Juda m’a oint pour son roi.
8 Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
Mais Abner, fils de Ner, prince de l’armée de Saül, prit Isboseth, fils de Saül, et lui fit parcourir le camp.
9 Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
Et il l’établit roi sur Galaad, sur Gessuri, sur Jezraël, sur Ephraïm, sur Benjamin et sur tout Israël.
10 Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
Isboseth, fils de Saül, avait quarante ans, lorsqu’il commença à régner sur Israël, et il régna deux ans; mais la seule maison de Juda suivait David.
11 Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
Et le nombre des jours que David demeura, régnant à Hébron sur la maison de Juda, fut de sept ans et six mois.
12 Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
Et Abner, fils de Ner, sortit du camp, et les serviteurs d’Isboseth, fils de Saül, pour venir à Gabaon.
13 Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
Mais Joab, fils de Sarvia, et les serviteurs de David sortirent, et les rencontrèrent près de la piscine de Gabaon. Et lorsqu’ils se furent assemblés, ils se postèrent en droite ligne, ceux-ci d’un côté de la piscine, et ceux-là de l’autre.
14 Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
Alors Abner dit à Joab: Que les jeunes hommes se lèvent, et qu’ils escarmouchent devant nous. Et Joab répondit: Qu’ils se lèvent.
15 Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
Ils se levèrent donc, et ils passèrent au nombre de douze de Benjamin, du côté d’Isboseth, fils de Saül, et de douze d’entre les serviteurs de David.
16 Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
Et chacun, ayant pris par la tête son concurrent, enfonça son glaive dans le côté de son adversaire, et ils tombèrent ensemble; et on appela ce lieu du nom de Champ des forts à Gabaon.
17 Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
Et il s’éleva une guerre très violente en ce jour-là; et Abner fut mis en fuite et les hommes d’Israël par les serviteurs de David.
18 ’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
Or étaient là les trois fils de Sarvia, Joab, Abisaï et Asaël; et Asaël fut un coureur très agile, comme un des chevreuils qui demeurent dans les forêts.
19 Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
Aussi Asaël poursuivait Abner, et il ne se détourna ni à droite ni à gauche, ne cessant de poursuivre Abner.
20 Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
C’est pourquoi Abner regarda derrière lui, et dit: Es-tu Asaël, toi? Et il répondit: Oui, je le suis.
21 Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
Et Abner lui dit: Va à droite ou à gauche, et saisis un de ces jeunes hommes et prends pour toi ses dépouilles. Mais Asaël ne voulut pas cesser de le poursuivre.
22 Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
Et Abner parla de nouveau à Asaël: Retire-toi, ne me suis point, pour ne pas que je sois forcé de te percer contre la terre; car je ne pourrai lever ma face du côté de Joab ton frère.
23 Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
Asaël dédaigna de l’entendre, et ne voulut pas se détourner. Abner donc, retournant sa lance, le frappa dans l’aîne, le transperça, et il mourut dans le même lieu; et tous ceux qui passaient par ce lieu dans lequel Asaël était tombé et était mort, s’arrêtaient.
24 Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
Or, Joab et Abisaï poursuivant Abner qui s’enfuyait, le soleil se coucha; et ils vinrent jusqu’à la colline de l’aqueduc, qui est vis-à-vis de la vallée, sur le chemin du désert de Gabaon.
25 Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
Et les enfants de Benjamin s’assemblèrent auprès d’Abner; et réunis en un seul bataillon, ils s’arrêtèrent sur le haut d’un tertre.
26 Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
Alors Abner cria à Joab, et dit: Est-ce jusqu’à la dernière extermination que ton glaive tranchant sévira? Ignores-tu que le désespoir est dangereux? Jusqu’à quand ne diras-tu pas au peuple, qu’il cesse de poursuivre ses frères?
27 Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
Et Joab lui répondit: Le Seigneur vit! si tu avais parlé, ce matin se serait retiré le peuple qui poursuit son frère.
28 Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
Joab donc sonna de la trompette, et toute l’armée s’arrêta; et ils ne poursuivirent plus Israël, et ils n’engagèrent pas le combat.
29 Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
Or, Abner et ses hommes s’en allèrent à travers les plaines, pendant toute cette nuit-là, et ils passèrent le Jourdain, et, tout Béthoron traversé, ils vinrent au camp.
30 Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
Quant à Joab, étant revenu, après avoir laissé Abner de côté, il assembla tout le peuple; et il manqua des serviteurs de David dix-neuf hommes, sans compter Asaël.
31 Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
Mais les serviteurs de David frappèrent de Benjamin et des hommes qui étaient avec Abner trois cent soixante, qui même moururent.
32 Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.
Et ils emportèrent Asaël, et l’ensevelirent dans le sépulcre de son père à Bethléhem; et Joab et les hommes qui étaient avec lui marchèrent pendant toute la nuit, et au point du jour ils parvinrent à Hébron.

< 2 Sama’ila 2 >