< 2 Sama’ila 2 >
1 Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
And it came to pass, after this, that David enquired of Yahweh, saying—Shall I go up into one of the cities of Judah? And Yahweh said unto him, Go up. And David said—Whither shall I go up? And he said—Unto Hebron.
2 Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
So David went up thither, and his two wives also, —Ahinoam, the Jezreelitess, and Abigail, wife of Nabal the Carmelite.
3 Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
His men also who were with him, did David bring up, every man with his household, —and they dwelt in the cities of Hebron.
4 Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
Then came the men of Judah, and anointed David there, to be king over the house of Judah. And they told David, saying, Men of Jabesh-gilead, were they who buried Saul.
5 sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
So David sent messengers unto the men of Jabesh-gilead, —and said unto them—Blessed, be ye of Yahweh, that ye did this lovingkindness unto your lord, unto Saul, and buried him.
6 Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
Now, therefore, Yahweh requite you with lovingkindness and truth, —moreover also, I, will requite you, for this noble deed, in that ye did this thing.
7 Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
Now, therefore, let your hands be made firm, and become ye sons of valour, for your lord Saul is dead, —and, me, moreover have the house of Judah anointed, to be king over them.
8 Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
But, Abner son of Ner, prince of the host that pertained unto Saul, took Ish-bosheth, son of Saul, and brought him over to Mahanaim;
9 Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
and made him king for Gilead, and for the Ashurites, and for Jezreel, —and over Ephraim, and over Benjamin, and over, all Israel.
10 Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
Forty years old, was Ish-bosheth son of Saul, when he began to reign over Israel, and, two years, reigned he, —but, the house of Judah, followed David.
11 Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
And it came to pass, that, the number of the days that David was king in Hebron, over the house of Judah, was seven years and six months.
12 Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
And Abner son of Ner, and the servants of Ish-bosheth, son of Saul, came out from Mahanaim to Gibeon.
13 Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
And, Joab son of Zeruiah, and the servants of David, went out from Hebron and met, by the pool of Gibeon, together, —and they sat down, these, by the pool, on the one side, and, those, by the pool, on the other side.
14 Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
Then said Abner unto Joab, Let the young men arise, I pray thee, and make sport before us. And Joab said—Let them arise.
15 Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
Then there arose, and went over by number, —twelve of Benjamin, pertaining to Ish-bosheth, son of Saul, and twelve, of the servants of David.
16 Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
And they caught every one his fellow by the head, with his sword in his fellow’s side, so they fell, together, —and that place was called Helkath-hazzadim ["Field of Plotters"], which is in Gideon.
17 Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
So the battle became exceeding obstinate, on that day, —and Abner and the men of Israel were defeated before the servants of David.
18 ’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
Now there were there, three sons of Zeruiah, Joab, and Abishai, and Asahel, —and, Asahel, was light of foot as a wild gazelle.
19 Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
And Asahel pursued Abner, —and turned not, in going, to the right hand or to the left, from pursuing Abner.
20 Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
Then Abner looked behind him, and said—Art thou Asahel? And he said—I am.
21 Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
Then Abner said to him—Turn thee aside, to thy right hand, or to thy left, and lay thee hold on one of the young men, and take thee his armour. But Asahel would not turn aside from pursuing him.
22 Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
And Abner said, yet again, unto Asahel, Turn thee aside from pursuing me, —wherefore should I smite thee to the earth? how then should I lift up my face unto Joab, thy brother?
23 Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
Howbeit he refused to turn aside, wherefore Abner smote him with the hinder end of the spear, in the belly, that the spear came out behind him, and he fell there, and died on the spot, —and so it was, that, as many as came up to the place where Asahel fell and died, stood still.
24 Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
Then Joab and Abishai pursued Abner, —but, the sun, had gone in by the time, they, had come as far as the hill of Ammah, that overlooketh Giah, by way of the wilderness of Gibeon.
25 Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
And, when the sons of Benjamin had gathered themselves together after Abner, and become one band, —and had taken their stand on the top of a certain hill,
26 Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
then Abner cried aloud unto Joab, and said—To the uttermost, must the sword devour? Dost thou not well know that, bitter, shall it be, in the latter end? How long, then, wilt thou not bid the people turn back from pursuing their own brethren?
27 Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
Then said Joab—As God liveth, surely, if thou hadst not spoken, then in the morning, the people would of themselves have gone up, every man from pursuing his brother.
28 Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
So Joab blew with the horn, and all the people stood still, and they neither pursued Israel further, —nor fought any more.
29 Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
And, Abner and his men, journeyed through the waste plain all that night, —and crossed the Jordan, and went through all the Bithron, and entered Mahanaim.
30 Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
And, Joab, returned from pursuing Abner, and, when he had gathered together all the people, there were missing of the servants of David—nineteen men, and Asahel;
31 Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
but, the servants of David, had smitten of Benjamin, of the men of Abner, —[so that] three hundred and sixty men, had died.
32 Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.
And they carried Asahel, and buried him in the grave of his father, which was in Bethlehem, —and Joab and his men journeyed all the night, and had daylight in Hebron.