< 2 Sama’ila 2 >

1 Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
Sometime after this, David asked the Lord, “Should I go to one of the towns of Judah?” “Yes, do it,” the Lord replied. “Which one should I go to?” David asked. “Go to Hebron,” said the Lord.
2 Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
So David moved there with his two wives, Ahinoam from Jezreel and Abigail, Nabal's widow from Carmel.
3 Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
He also brought the men who were with him, along with their families, and they settled in the villages near Hebron.
4 Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
Then the men of Judah came to Hebron, and there they anointed David king of the people of Judah. When David found out that it was the men from Jabesh Gilead who had buried Saul,
5 sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
he sent messengers to them, saying, “May the Lord bless you, because you demonstrated your loyal love to Saul your master, and you buried him properly.
6 Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
Now may the Lord show you loyal love and trustworthiness, and I will also be good to you because of what you did for Saul.
7 Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
So be strong and be brave, for even though Saul your master is dead, the people of Judah have anointed me as their king.”
8 Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
However, Abner, son of Ner, commander of Saul's army, had taken Ishbosheth, son of Saul, to Mahanaim.
9 Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
There he set up Ishbosheth as king over Gilead, Asher, Jezreel, Ephraim, and Benjamin, in fact over all Israel.
10 Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
Ishbosheth, son of Saul, was forty when he became king over Israel, and he reigned for two years. However, the people of Judah were on David's side.
11 Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
David ruled in Hebron as king over the people of Judah for seven years and six months.
12 Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
One day Abner and Ishbosheth's men left Mahanaim and went to the town of Gibeon.
13 Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
Joab, son of Zeruiah, and David's men set off and met them at the pool of Gibeon, where they all sat down, facing each other across the pool.
14 Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
Abner said to Joab, “Why not let's have some of the men fight in hand to hand combat before us.” “Fine,” Joab agreed.
15 Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
So twelve men came forward from each side—twelve for Benjamin and Ishbosheth, and twelve for David.
16 Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
Each man grabbed his opponent's head and drove his sword into his opponent's side so that they all fell down dead together. That's why this place in Gibeon is called the Field of Sword-edges.
17 Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
The battle that followed was hard-fought, but eventually Abner and his men were defeated by David's men.
18 ’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
The three sons of Zeruiah were there: Joab, Abishai, and Asahel. Asahel was a fast runner, like a gazelle racing across the open countryside.
19 Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
He chased after Abner with single-minded determination.
20 Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
Abner looked back and asked, “Is that you, Asahel?” “Yes, it's me,” Asahel replied.
21 Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
Abner told him, “Leave me alone! Go and fight somebody else and take his weapons for yourself!” But Asahel refused to stop chasing him.
22 Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
Abner warned Asahel again. “Stop chasing me!” he shouted. “Why do you want me to kill you? How could I ever face your brother Joab?”
23 Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
But Asahel wouldn't stop chasing him, so Abner drove the handle of his spear into his belly. It came out the back, and he fell down dead right there. Everyone who passed by stopped at the place where Asahel had fallen and died.
24 Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
But Joab and Abishai set off to chase after Abner. By the time the sun went down they had got as far as the hill of Ammah near Giah, on the way to the wilderness of Gibeon.
25 Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
Abner's men from the tribe of Benjamin rallied to him there, forming a tight group around him standing at the top of the hill.
26 Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
Abner shouted to Joab: “Do we have to keep killing each other forever? Don't you realize that if we go on it'll only get worse? How long are you going to wait before you order your men to stop chasing their brothers?”
27 Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
“As God lives,” Joab replied, “if you had not said anything, my men would have continued chasing their brothers until the morning.”
28 Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
Joab blew the horn so all the men stopped—they didn't continue chasing or fighting the Israelites.
29 Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
All through the night Abner and his men marched through the Jordan Valley. They crossed the Jordan River, and continued all morning until they arrived back at Mahanaim.
30 Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
When Joab got back from chasing Abner, he gathered all the men together. Nineteen of David's men were missing in addition to Asahel.
31 Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
However, they had killed three hundred and sixty of Abner's men from the tribe of Benjamin.
32 Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.
They took Asahel's body and buried him in his father's tomb in Bethlehem. Then they marched all through the night and reached Hebron at dawn.

< 2 Sama’ila 2 >