< 2 Sama’ila 19 >
1 Aka faɗa wa Yowab cewa, “Sarki yana kuka, yana kuma makoki saboda Absalom.”
Och det vardt bådadt Joab: Si, Konungen gråter, och beklagar sig om Absalom.
2 Saboda haka sai nasarar da aka yi a ranar ta zama makoki ga dukan sojoji, gama a ranar, rundunoni sun ji an ce, “Sarki yana baƙin ciki domin ɗansa.”
Och vardt i den dagen en sorg af segren i hela folkena; förty folket hade i den dagen hört, att Konungen var bedröfvad om sin son.
3 Mutane fa suka shiga birni shiru, sai ka ce waɗanda sukan sace jiki don kunya sa’ad da suka gudo daga yaƙi.
Och folket drog sig bort i den dagen, så att det icke kom i staden, lika som ett folk drager sig bort, som till blygd kommet är, när det i strid flytt hafver.
4 Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da ƙarfi yana cewa, “Ya ɗana Absalom! Ya Absalom ɗana, ɗana!”
Men Konungen förskylde sitt ansigte, och ropade högt: Ack! min son Absalom! Absalom, min son, min son!
5 Sai Yowab ya shiga gidan sarki ya ce, “Yau ka kunyatar da dukan mutanenka, waɗanda ba da daɗewa ba sun ceci ranka, da rayukan’ya’yanka maza, da na’ya’yanka mata, da na matanka da kuma na ƙwarƙwaranka.
Så gick Joab in uti huset till Konungen, och sade: Du hafver i dag till blygd gjort alla dina tjenare, som i dag undsatt hafva dina, dina söners, dina döttrars, dina hustrurs och dina frillors själar;
6 Kana ƙaunar maƙiyinka, kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Ka bayyana a fili cewa komandodi da sojojinsu ba kome ba ne a gare ka. Na ga cewa da za ka yi farin ciki, da a ce Absalom yana da rai a yau, dukanmu kuma mun mutu.
Så att du hafver dem kär som dig hata, och hatar dem som dig kär hafva; ty du låter dig märka i dag, att dig ligger ingen magt uppå höfvitsmännerna och tjenarena; utan jag märker i dag väl, att om allenast Absalom lefde dig, och vi alle i dag döde vore, det skulle dig tycka så godt vara.
7 Yanzu ka fita ka ƙarfafa mutanenka. Na rantse da Ubangiji, in ba ka fita ba, babu mutum guda da za a bari tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni fiye da kowace irin masifar da ta auko maka tun ƙuruciyarka har zuwa yanzu.”
Så statt nu upp, och gack ut, och tala vänliga med dina tjenare; ty jag svär dig vid Herran: Om du icke går ut, blifver icke en man qvar när dig öfver denna nattena; det skall vara dig värre, än allt det onda som öfver dig kommet är, ifrå din ungdom allt intill nu.
8 Saboda haka sarki ya tashi, ya zauna a bakin hanyar shiga. Da aka faɗa wa mutane cewa, “Sarki yana zaune a bakin hanyar shiga,” sai duk suka zo gabansa. Ana cikin haka, Isra’ilawa dai sun riga sun tsere zuwa gidajensu.
Då stod Konungen upp, och satte sig i porten, och allo folkena vardt sagdt: Si, Konungen sitter i portenom. Så kom allt folket för Konungen; men Israel var flydd, hvar och en i sin hyddo.
9 Mutane ko’ina a kabilan Isra’ila, suka yi ta gardama da juna, suna cewa, “Sarki ne ya cece mu daga hannun abokan gābanmu, shi ne kuma ya kuɓutar da mu daga hannun Filistiyawa. Amma ga shi ya tsere daga ƙasar saboda Absalom;
Och allt folket kifvade tillhopa i alla Israels slägter, och sade: Konungen hafver hulpit oss utu våra fiendars hand, och förlossat oss utu de Philisteers hand, och hafver måst fly utaf landena för Absalom.
10 kuma shi Absalom, da muka naɗa yă yi mulkinmu, ya mutu a yaƙi. Saboda haka don me ba kwa ce wani abu game da dawo da sarki?”
Så är Absalom död blifven i stridene, den vi öfver oss smort hade; hvi ären I nu så stilla, att I icke hemten Konungen igen?
11 Sai Sarki Dawuda ya aika da saƙo zuwa wurin Zadok da Abiyatar, firistoci, ya ce, “Ku tambayi dattawan Yahuda, ‘Me ya sa ku ne za ku zama na ƙarshe a yin tunanin komar da sarki zuwa fada, da yake abin da ake faɗi ko’ina a Isra’ila ya kai kunnen sarki a mazauninsa?
Och Konungen sände till Zadok och AbJathar Presterna, och lät säga dem: Taler med de äldsta i Juda, och säger: Hvi viljen I vara de siste, till att hemta Konungen hem i sitt hus igen? Ty hela Israels tal var kommet för Konungen i hans hus.
12 Ku’yan’uwana ne, jikina, jinina kuma. To, don me za ku zama na ƙarshe na yarda a dawo da sarki zuwa fada?’
I ären mine bröder, mitt ben, och mitt kött; hvi viljen I då vara de siste, till att hemta Konungen igen?
13 Ku kuma ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba jikina ba ne da jinina? Allah yă hukunta ni, da hukunci mai tsanani, idan daga yanzu ba ka zama komandan sojojina a maimakon Yowab ba.’”
Och till Amasa säger: Äst du icke mitt ben, och mitt kött? Gud göre mig det och det, om du icke skall blifva härhöfvitsman för mig, så länge du lefver, i Joabs stad.
14 Ta haka ya rinjayi zukatan dukan mutane Yahuda, kamar mutum ɗaya. Suka aika da saƙo wurin sarki suka ce, “Ka dawo, kai da dukan mutanenka.”
Och han bevekte alla Juda mäns hjerta, såsom ens mans; och de sände till Konungen: Kom igen, du och alle dine tjenare.
15 Sa’an nan sarki ya dawo, ya kuma tafi har zuwa Urdun. To, mutanen Yahuda suka zo Gilgal don su fita su taryi sarki, su kuma kawo shi ƙetaren Urdun.
Så kom då Konungen igen. Och som han kom till Jordan, voro Juda män komne till Gilgal, till att draga neder emot Konungen, att de skulle föra Konungen öfver Jordan.
16 Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuda don su taryi Sarki Dawuda.
Och Simei, Gera son, Jemini sons, som i Bahurim bodde, hastade sig, och drog neder med Juda män emot Konung David.
17 Tare da shi akwai kabilar Benyamin mutum dubu, tare da Ziba, mai hidimar gidan Shawulu, da’ya’yansa maza goma sha biyar, da bayi ashirin. Suka ruga zuwa Urdun, inda sarki yake.
Och med honom voro tusende män af BenJamin; desslikes ock Ziba, den tjenaren af Sauls hus, med hans femton söner, och tjugu tjenare, och de skyndade sig öfver Jordan;
18 Suka haye a mashigin don su ƙetaro da iyalin sarki, su kuma yi duk abin da yake so. Sa’ad da Shimeyi ɗan Gera ya haye Urdun, sai ya fāɗi rubda ciki a gaban sarki
Och beredde färjona för Konungenom, att de skulle föra Konungens tjenare öfver, och göra det honom till vilja var. Och Simei, Gera son, föll neder för Konungen, då han for öfver Jordan;
19 ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka riƙe laifina a zuciya. Kada ka tuna da laifin da na yi maka ranka yă daɗe, ranan nan da kake gudu daga Urushalima. Kada ka tuna da shi ko kaɗan.
Och sade till Konungen: Min Herre, tillräkna mig icke den missgerning, och kom icke ihåg, att din tjenare förtörnade dig den dagen, då min herre Konungen gick utu Jerusalem, och Konungen lägge ett icke på hjertat;
20 Na sani ni bawanka na yi maka laifi. Shi ya sa na zama na farko daga dukan Gidan Yusuf, da mutanen Isra’ila wanda ya fito don yă tarye ka yau, ranka yă daɗe, sarki.”
Ty din tjenare känner, att jag syndat hafver. Och si, jag är i dag den förste kommen utaf Josephs hus, att jag skulle draga neder emot min herra Konungen.
21 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce, “Bai kamata a kashe Shimeyi saboda wannan ba? Ya la’anci shafaffe na Ubangiji.”
Men Abisai, ZeruJa son, svarade, och sade: Och skulle icke Simei derföre dö, som bannade Herrans smorda?
22 Dawuda ya ce, “Me ya haɗa ni da ku, ku’ya’yan Zeruhiya? Yau ɗin nan kun zama maƙiyana! Ya kamata a kashe wani a Isra’ila a yau? Ban san cewa yau ni sarki ne a bisa Isra’ila ba?”
David sade: Hvad hafver jag beställa med eder, I ZeruJa barn, att I viljen i dag varda mig till Satan? Skulle i dag någor dö i Israel? Menar du att jag icke vet, att jag i dag är vorden Konung öfver Israel?
23 Saboda haka sarki ya ce wa Shimeyi, “Ba za ka mutu ba.” Sarki kuwa ya yi alkawari har da rantsuwa.
Och Konungen sade till Simei: Du skall icke dö; och Konungen svor honom.
24 Mefiboshet, jikan Shawulu, shi ma ya gangara don yă taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har ran da ya komo lafiya, Mefiboshet bai lura da ƙafafunsa, ko yă aske gemunsa, ko yă wanke tufafinsa ba.
Kom också MephiBoseth, Sauls son, neder emot Konungen, och hade intet ryktat sina fötter, eller sitt skägg, eller tvagit sin kläder, ifrå den dagen Konungen bortgången var, intill den dagen då han kom med frid.
25 Sa’ad da ya zo daga Urushalima don yă taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba Mefiboshet?”
Då han nu till Jerusalem kom, till att möta Konungenom, sade Konungen till honom: Hvi for du icke med mig, MephiBoseth?
26 Sai ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, da yake bawanka gurgu ne, na ce, ‘A sa mini sirdi a kan jakina don in hau in tafi tare da sarki.’ Amma Ziba bawana ya bashe ni.
Och han sade: Min herre Konung, min tjenare gjorde orätt emot mig; ty din tjenare tänkte: Jag vill sadla en åsna, och stiga deruppå, och rida till min herra Konungen; förty din tjenare är ofärdig.
27 Ya kuwa ɓata suna bawanka a gaban ranka yă daɗe, sarki. Ranka yă daɗe, sarki yana kama da mala’ikan Allah, ka yi abin da ka ga ya fi maka kyau.
Dertill hafver han ock beklagat din tjenare för min herra Konungenom; men min herre Konungen är såsom en Guds Ängel, och må göra hvad honom täckes.
28 Duk zuriyar kakana ba su cancanci kome ba sai mutuwa daga ranka yă daɗe, amma ka ba wa bawanka wuri cikin mutanen da suke ci a teburinka. Saboda haka, wanda’yanci nake da shi da zan yi wani ƙarin roƙo a wurin sarki?”
Ty allt mins faders hus hafver icke varit utan till döden skyldigt för minom herra Konungenom; så hafver du dock satt din tjenare ibland dem, som äta öfver ditt bord; hvad rätt hafver jag mer, eller hvad kan jag mer ropa till Konungen?
29 Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”
Konungen sade till honom: Hvad talar du mer härom? Jag hafver sagt det, du och Ziba skifter åkren med hvarannan.
30 Mefiboshet ya ce wa sarki, “Bari yă ɗauki kome, yanzu da ranka yă daɗe, sarki ya dawo gida lafiya.”
MephiBoseth sade till Konungen: Han må tagan allsamman, efter min herre Konungen med frid hemkommen är.
31 Barzillai mutumin Gileyad shi ma ya zo daga Rogelim don yă ƙetare Urdun tare da sarki, yă kuma sallame shi daga can.
Och Barsillai, den Gileaditen, kom neder ifrå Roglim, och for öfver Jordan för Konungen, på det han skulle ledsaga honom öfver Jordan.
32 To, Barzillai fa tsoho ne, mai shekara tamanin. Ya tanada wa sarki a lokaci da yake Mahanayim, gama shi attajiri ne.
Och Barsillai var fast gammal, väl åttatio år; han hade försörjt Konungen, medan han var i Mahanaim; ty han var en ganska väldig man.
33 Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka ƙetaro tare da ni ka zauna tare da ni a Urushalima, zan kuwa tanada maka.”
Och Konungen sade till Barsillai: Du skall draga fram med mig; jag vill försörja dig med mig i Jerusalem.
34 Amma Barzillai ya ce wa sarki, “Shekara nawa ya rage mini har da zan tafi Urushalima da sarki?
Men Barsillai sade till Konungen: Hvad är det jag ännu hafver till att lefva, att jag ännu skulle draga upp med Konungenom till Jerusalem?
35 Yanzu ina da shekara tamanin. Zan iya bambanta abu mai daɗi da marar daɗi kuma ne? Bawanka zai iya jin ɗanɗano abin da yake ci, ko yake sha ne? Har yanzu zan iya jin muryoyin mawaƙan maza da mata? Don me bawanka zai zama ƙari kaya ga ranka yă daɗe?
Jag är i dag åttatio år gammal; huru skulle jag känna hvad godt eller ondt är? Eller smaka hvad jag äter eller dricker? Eller höra hvad de sångare eller sångerskor sjunga? Hvi skulle din tjenare ytterligare besvära min herra Konungen?
36 Bawanka zai ƙetare Urdun tare da sarki, yă ɗan yi maka rakiya kaɗan. Me ya sa ranka yă daɗe zai ba ni irin wannan lada.
Din tjenare skall något litet fara med Konungenom öfver Jordan; hvi skulle Konungen göra mig en sådana vedergällning?
37 Ka bar bawanka yă koma, don in mutu a garina, kusa da kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ga bawanka Kimham. Bari yă ƙetare tare da ranka yă daɗe, sarki. Ka yi abin da ka ga dama da shi.”
Låt din tjenare vända om igen, att jag må dö i minom stad, och varda begrafven i mins faders och mine moders grift. Si, der är din tjenare Chimham, den låt draga öfver med min herra Konungen; och gör honom hvad dig täckes.
38 Sarki ya ce, “Kimham zai ƙetare tare da ni, zan kuwa yi masa abin da ya gamshe ka. Kuma duk abin da kake bukata a wurina, zan yi maka.”
Konungen sade: Chimham skall draga öfver med mig, och jag vill göra honom hvad dig är till vilja; och allt det du bedes af mig, det vill jag göra dig.
39 Saboda haka dukan mutane suka ƙetare Urdun, sa’an nan kuma sarki ma ya ƙetare. Sarki ya yi wa Barzillai sumba ya albarkace shi, sa’an nan Barzillai ya koma gidansa.
Och då allt folket var kommet öfver Jordan, och Konungen desslikes, kysste Konungen Barsillai, och välsignade honom; och han vände om igen till sitt rum.
40 Sa’ad da sarki ya ƙetare zuwa Gilgal, Kimham ma ya ƙetare tare da shi. Dukan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra’ila suka ƙetare da sarki.
Och Konungen drog öfver till Gilgal, och Chimham for med honom; och allt Juda folk hade fört Konungen öfver; men Israels folk var icke utan hälften der.
41 Nan take sai ga mutane Isra’ila suna zuwa wurin sarki, suna cewa, “Don me’yan’uwanmu, mutanen Yahuda, suka saci sarki, suka kawo shi da iyalinsa a ƙetaren Urdun, tare da dukan mutanensa?”
Och si, då kommo alle Israels män till Konungen, och sade till honom: Hvi hafva våre bröder, Juda män, stulit dig, och hafva fört Konungen och hans hus öfver Jordan, och alla Davids män med honom?
42 Dukan mutanen Yahuda suka ce wa mutanen Isra’ila, “Mun yi haka domin sarki danginmu na kurkusa ne. Don me kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abu daga cikin kayan sarki ne? Mun ɗauki wani abu wa kanmu ne?”
Då svarade de af Juda dem af Israel: Konungen är oss när åkommen; hvi ären I der vrede före? Menen I, att vi af Konungenom kost och skänker fått hafve?
43 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka ce wa mutanen Yahuda, “Muna da rabo goma a wurin sarki; ban da haka ma, muna da hakki mafi yawa a wurin Dawuda fiye da ku. Don me kuke mana reni? Ba mu ne ma muka fara magana dawowa da sarki ba?” Amma mutanen Yahuda suka ɗauka maganar da zafi fiye da mutanen Isra’ila.
Så svarade då de af Israel dem af Juda, och sade: Vi hafve tio sinom mer, med Konungenom, med David också, än I; hvi hafver du då så ringa aktat mig, att vi icke måtte hafva varit de förste, till att hemta vår Konung? Men de af Juda talade hårdare, än de män af Israel.