< 2 Sama’ila 19 >

1 Aka faɗa wa Yowab cewa, “Sarki yana kuka, yana kuma makoki saboda Absalom.”
به یوآب خبر دادند که پادشاه برای ابشالوم عزا گرفته است و گریه می‌کند.
2 Saboda haka sai nasarar da aka yi a ranar ta zama makoki ga dukan sojoji, gama a ranar, rundunoni sun ji an ce, “Sarki yana baƙin ciki domin ɗansa.”
وقتی مردم شنیدند که پادشاه برای پسرش غصه‌دار است، شادی پیروزی بزرگ آن روز ایشان، به غم مبدل شد.
3 Mutane fa suka shiga birni shiru, sai ka ce waɗanda sukan sace jiki don kunya sa’ad da suka gudo daga yaƙi.
سربازان مثل نیروی شکست خورده بی‌سر و صدا و با سرهای افکنده وارد شهر شدند.
4 Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da ƙarfi yana cewa, “Ya ɗana Absalom! Ya Absalom ɗana, ɗana!”
پادشاه صورت خود را با دستهایش پوشانده بود و به تلخی می‌گریست و می‌گفت: «ای پسرم ابشالوم، ای پسرم ابشالوم، ای پسرم!»
5 Sai Yowab ya shiga gidan sarki ya ce, “Yau ka kunyatar da dukan mutanenka, waɗanda ba da daɗewa ba sun ceci ranka, da rayukan’ya’yanka maza, da na’ya’yanka mata, da na matanka da kuma na ƙwarƙwaranka.
یوآب به خانهٔ پادشاه رفت و به او گفت: «ما امروز جان تو و زندگی پسران و دختران، زنان و کنیزانت را نجات دادیم؛ ولی تو با این رفتار خود ما را تحقیر کردی.
6 Kana ƙaunar maƙiyinka, kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Ka bayyana a fili cewa komandodi da sojojinsu ba kome ba ne a gare ka. Na ga cewa da za ka yi farin ciki, da a ce Absalom yana da rai a yau, dukanmu kuma mun mutu.
اینطور که به نظر می‌رسد تو کسانی را دوست داری که از تو متنفرند و از کسانی نفرت داری که دوستت دارند. گویی سرداران و افرادت برای تو هیچ ارزش ندارند. اگر ابشالوم زنده می‌ماند و همهٔ ما می‌مردیم، تو خوشحال می‌شدی.
7 Yanzu ka fita ka ƙarfafa mutanenka. Na rantse da Ubangiji, in ba ka fita ba, babu mutum guda da za a bari tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni fiye da kowace irin masifar da ta auko maka tun ƙuruciyarka har zuwa yanzu.”
حال، بلند شو و بیرون بیا و به سربازانت تبریک بگو. به خداوند زنده قسم اگر چنین نکنی، امشب حتی یکی از آنها در اینجا باقی نخواهد ماند، و این از تمام بلاهایی که تاکنون برایت پیش آمده، بدتر خواهد بود.»
8 Saboda haka sarki ya tashi, ya zauna a bakin hanyar shiga. Da aka faɗa wa mutane cewa, “Sarki yana zaune a bakin hanyar shiga,” sai duk suka zo gabansa. Ana cikin haka, Isra’ilawa dai sun riga sun tsere zuwa gidajensu.
پس پادشاه بیرون رفته، کنار دروازهٔ شهر نشست. وقتی افرادش این را شنیدند، دورش جمع شدند. در ضمن، تمام سربازان اسرائیلی به خانه‌های خود گریخته بودند.
9 Mutane ko’ina a kabilan Isra’ila, suka yi ta gardama da juna, suna cewa, “Sarki ne ya cece mu daga hannun abokan gābanmu, shi ne kuma ya kuɓutar da mu daga hannun Filistiyawa. Amma ga shi ya tsere daga ƙasar saboda Absalom;
در سراسر مملکت، این بحث درگرفته بود که چرا نمی‌رویم پادشاه خود را که به سبب ابشالوم از مملکت فرار کرده، باز گردانیم؟ او بود که ما را از شر دشمنان فلسطینی نجات داد. ابشالوم هم که به جای پدرش به پادشاهی انتخاب کردیم، اینک مرده است. پس بیایید داوود را باز گردانیم تا دوباره پادشاه ما شود.
10 kuma shi Absalom, da muka naɗa yă yi mulkinmu, ya mutu a yaƙi. Saboda haka don me ba kwa ce wani abu game da dawo da sarki?”
11 Sai Sarki Dawuda ya aika da saƙo zuwa wurin Zadok da Abiyatar, firistoci, ya ce, “Ku tambayi dattawan Yahuda, ‘Me ya sa ku ne za ku zama na ƙarshe a yin tunanin komar da sarki zuwa fada, da yake abin da ake faɗi ko’ina a Isra’ila ya kai kunnen sarki a mazauninsa?
داوود، صادوق و اَبیّاتار کاهن را فرستاد تا به بزرگان یهودا بگویند: «چرا شما در باز آوردن پادشاه، آخر همه هستید؟ تمام قوم اسرائیل آمادهٔ حرکتند به‌جز شما که برادران و قبیله و گوشت و خون من هستید.»
12 Ku’yan’uwana ne, jikina, jinina kuma. To, don me za ku zama na ƙarshe na yarda a dawo da sarki zuwa fada?’
13 Ku kuma ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba jikina ba ne da jinina? Allah yă hukunta ni, da hukunci mai tsanani, idan daga yanzu ba ka zama komandan sojojina a maimakon Yowab ba.’”
در ضمن، به صادوق و اَبیّاتار گفت که به عماسا بگویند: «تو خویشاوند من هستی، پس خدا مرا بزند اگر تو را به جای یوآب به فرماندهی سپاه خود نگمارم.»
14 Ta haka ya rinjayi zukatan dukan mutane Yahuda, kamar mutum ɗaya. Suka aika da saƙo wurin sarki suka ce, “Ka dawo, kai da dukan mutanenka.”
پیغام داوود تمام قبیله یهودا را خشنود کرد و آنها با دل و جان جواب مثبت داده، برای پادشاه پیغام فرستادند که همراه افرادش پیش آنها بازگردد.
15 Sa’an nan sarki ya dawo, ya kuma tafi har zuwa Urdun. To, mutanen Yahuda suka zo Gilgal don su fita su taryi sarki, su kuma kawo shi ƙetaren Urdun.
پس پادشاه عازم پایتخت شد. وقتی به رود اردن رسید تمام مردم یهودا برای استقبالش به جلجال آمدند تا او را از رود اردن عبور دهند.
16 Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuda don su taryi Sarki Dawuda.
آنگاه شمعی (پسر جیرای بنیامینی) که از بحوریم بود، با عجله همراه مردان یهودا به استقبال داوود پادشاه رفت.
17 Tare da shi akwai kabilar Benyamin mutum dubu, tare da Ziba, mai hidimar gidan Shawulu, da’ya’yansa maza goma sha biyar, da bayi ashirin. Suka ruga zuwa Urdun, inda sarki yake.
هزار نفر از قبیلهٔ بنیامین و صیبا خدمتگزار خاندان شائول با پانزده پسرش و بیست نوکرش همراه شمعی بودند. آنها قبل از پادشاه به رود اردن رسیدند.
18 Suka haye a mashigin don su ƙetaro da iyalin sarki, su kuma yi duk abin da yake so. Sa’ad da Shimeyi ɗan Gera ya haye Urdun, sai ya fāɗi rubda ciki a gaban sarki
بعد، از رودخانه گذشتند تا خاندان سلطنتی را به آن طرف رودخانه بیاورند و هر چه خواست پادشاه باشد، انجام دهند. پیش از اینکه پادشاه از رودخانه عبور کند، شمعی در برابر او به خاک افتاد
19 ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka riƙe laifina a zuciya. Kada ka tuna da laifin da na yi maka ranka yă daɗe, ranan nan da kake gudu daga Urushalima. Kada ka tuna da shi ko kaɗan.
و گفت: «ای پادشاه، التماس می‌کنم مرا ببخشید و فراموش کنید آن رفتار زشتی را که هنگام بیرون آمدنتان از اورشلیم، مرتکب شدم.
20 Na sani ni bawanka na yi maka laifi. Shi ya sa na zama na farko daga dukan Gidan Yusuf, da mutanen Isra’ila wanda ya fito don yă tarye ka yau, ranka yă daɗe, sarki.”
چون خودم خوب می‌دانم که چه اشتباه بزرگی مرتکب شده‌ام! به همین دلیل هم امروز زودتر از تمام افراد قبیلهٔ یوسف آمده‌ام تا به پادشاه خوش آمد بگویم.»
21 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce, “Bai kamata a kashe Shimeyi saboda wannan ba? Ya la’anci shafaffe na Ubangiji.”
ابیشای پسر صرویه گفت: «آیا شمعی به سبب اینکه به پادشاه برگزیدهٔ خداوند ناسزا گفت، نباید کشته شود؟»
22 Dawuda ya ce, “Me ya haɗa ni da ku, ku’ya’yan Zeruhiya? Yau ɗin nan kun zama maƙiyana! Ya kamata a kashe wani a Isra’ila a yau? Ban san cewa yau ni sarki ne a bisa Isra’ila ba?”
داوود جواب داد: «ای پسران صرویه، چرا در کار من دخالت می‌کنید؟ چرا می‌خواهید دردسر ایجاد کنید؟ امروز در اسرائیل منم که سلطنت می‌کنم، پس نباید کسی کشته شود!»
23 Saboda haka sarki ya ce wa Shimeyi, “Ba za ka mutu ba.” Sarki kuwa ya yi alkawari har da rantsuwa.
سپس رو به شمعی کرد و قسم خورده، گفت: «تو کشته نخواهی شد.»
24 Mefiboshet, jikan Shawulu, shi ma ya gangara don yă taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har ran da ya komo lafiya, Mefiboshet bai lura da ƙafafunsa, ko yă aske gemunsa, ko yă wanke tufafinsa ba.
در این بین، مفیبوشت، نوهٔ شائول از اورشلیم به استقبال پادشاه آمد. از روزی که پادشاه از پایتخت رفته بود، مفیبوشت پاها و لباسهای خود را نشسته بود و سر و صورتش را نیز اصلاح نکرده بود. پادشاه از او پرسید: «ای مفیبوشت، چرا همراه من نیامدی؟»
25 Sa’ad da ya zo daga Urushalima don yă taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba Mefiboshet?”
26 Sai ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, da yake bawanka gurgu ne, na ce, ‘A sa mini sirdi a kan jakina don in hau in tafi tare da sarki.’ Amma Ziba bawana ya bashe ni.
عرض کرد: «ای پادشاه، صیبا، خادم من، مرا فریب داد. به او گفتم که الاغم را آماده کند تا بتوانم همراه پادشاه بروم، ولی او این کار را نکرد. چنانکه می‌دانید من لنگ هستم.
27 Ya kuwa ɓata suna bawanka a gaban ranka yă daɗe, sarki. Ranka yă daɗe, sarki yana kama da mala’ikan Allah, ka yi abin da ka ga ya fi maka kyau.
در عوض مرا متهم کرده است به اینکه نخواسته‌ام همراه شما بیایم. اما من می‌دانم شما مثل فرشتهٔ خدا هستید. پس هر چه می‌خواهید با من بکنید.
28 Duk zuriyar kakana ba su cancanci kome ba sai mutuwa daga ranka yă daɗe, amma ka ba wa bawanka wuri cikin mutanen da suke ci a teburinka. Saboda haka, wanda’yanci nake da shi da zan yi wani ƙarin roƙo a wurin sarki?”
«من و همهٔ بستگانم می‌بایست به دست پادشاه کشته می‌شدیم، ولی در عوض به من افتخار دادید بر سر سفره‌تان خوراک بخورم! پس من چه حق دارم از پادشاه توقع بیشتری داشته باشم؟»
29 Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”
پادشاه گفت: «لازم نیست این چیزها را بگویی. دستور داده‌ام تو و صیبا، مِلک شائول را بین خودتان تقسیم کنید.»
30 Mefiboshet ya ce wa sarki, “Bari yă ɗauki kome, yanzu da ranka yă daɗe, sarki ya dawo gida lafiya.”
مفیبوشت عرض کرد: «ای آقا، تمام ملک را به او بدهید. همین که می‌بینم پادشاه به سلامت به خانه بازگشته برای من کافی است!»
31 Barzillai mutumin Gileyad shi ma ya zo daga Rogelim don yă ƙetare Urdun tare da sarki, yă kuma sallame shi daga can.
برزلائی که از داوود و سربازان او در طی مدتی که در محنایم بودند پذیرایی می‌کرد، از روجلیم آمد تا پادشاه را تا آن طرف رود اردن مشایعت کند. او پیرمردی هشتاد ساله و بسیار ثروتمند بود.
32 To, Barzillai fa tsoho ne, mai shekara tamanin. Ya tanada wa sarki a lokaci da yake Mahanayim, gama shi attajiri ne.
33 Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka ƙetaro tare da ni ka zauna tare da ni a Urushalima, zan kuwa tanada maka.”
پادشاه به او گفت: «همراه من بیا و در اورشلیم زندگی کن. من در آنجا از تو نگه داری می‌کنم.»
34 Amma Barzillai ya ce wa sarki, “Shekara nawa ya rage mini har da zan tafi Urushalima da sarki?
برزلائی جواب داد: «مگر از عمرم چقدر باقی است که همراه تو به اورشلیم بیایم؟
35 Yanzu ina da shekara tamanin. Zan iya bambanta abu mai daɗi da marar daɗi kuma ne? Bawanka zai iya jin ɗanɗano abin da yake ci, ko yake sha ne? Har yanzu zan iya jin muryoyin mawaƙan maza da mata? Don me bawanka zai zama ƙari kaya ga ranka yă daɗe?
الان هشتاد ساله هستم و نمی‌توانم از چیزی لذت ببرم. خوراک و شراب دیگر برایم مزه‌ای ندارد. صدای ساز و آواز نیز گوشم را نوازش نمی‌دهد. بنابراین، برای پادشاه باری خواهم بود.
36 Bawanka zai ƙetare Urdun tare da sarki, yă ɗan yi maka rakiya kaɗan. Me ya sa ranka yă daɗe zai ba ni irin wannan lada.
همین قدر که می‌توانم همراه شما به آن طرف رودخانه بیایم، برای من افتخار بزرگی است.
37 Ka bar bawanka yă koma, don in mutu a garina, kusa da kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ga bawanka Kimham. Bari yă ƙetare tare da ranka yă daɗe, sarki. Ka yi abin da ka ga dama da shi.”
اجازه دهید به شهر خود برگردم و در کنار پدر و مادرم دفن بشوم. ولی پسرم کمهام اینجاست؛ اجازه بفرمایید او همراه شما بیاید تا پادشاه هر چه صلاح می‌داند در مورد او انجام دهد.»
38 Sarki ya ce, “Kimham zai ƙetare tare da ni, zan kuwa yi masa abin da ya gamshe ka. Kuma duk abin da kake bukata a wurina, zan yi maka.”
پادشاه قبول کرد و گفت: «بسیار خوب، او را همراه خود می‌برم و هر چه تو صلاح بدانی برای او می‌کنم. آنچه بخواهی برای تو انجام می‌دهم.»
39 Saboda haka dukan mutane suka ƙetare Urdun, sa’an nan kuma sarki ma ya ƙetare. Sarki ya yi wa Barzillai sumba ya albarkace shi, sa’an nan Barzillai ya koma gidansa.
پس تمام مردم با پادشاه از رود اردن عبور کردند. آنگاه داوود برزلائی را بوسید و برایش دعای برکت کرد و او به خانه‌اش بازگشت.
40 Sa’ad da sarki ya ƙetare zuwa Gilgal, Kimham ma ya ƙetare tare da shi. Dukan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra’ila suka ƙetare da sarki.
سپس داوود به جلجال رفت و کمهام را نیز با خود برد. تمام قبیلهٔ یهودا و نصف اسرائیل در عبور دادن پادشاه از رودخانه شرکت داشتند.
41 Nan take sai ga mutane Isra’ila suna zuwa wurin sarki, suna cewa, “Don me’yan’uwanmu, mutanen Yahuda, suka saci sarki, suka kawo shi da iyalinsa a ƙetaren Urdun, tare da dukan mutanensa?”
ولی مردان اسرائیل به پادشاه شکایت نمودند که چرا مردان یهودا پیش دستی کرده‌اند تا فقط خودشان پادشاه و خاندان و افراد او را از رودخانه عبور دهند؟
42 Dukan mutanen Yahuda suka ce wa mutanen Isra’ila, “Mun yi haka domin sarki danginmu na kurkusa ne. Don me kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abu daga cikin kayan sarki ne? Mun ɗauki wani abu wa kanmu ne?”
مردان یهودا جواب دادند: «ما حق داشتیم این کار را بکنیم، چون پادشاه از قبیلهٔ ماست. چرا شما از این موضوع ناراحتید؟ پادشاه به ما نه خوراکی داده است و نه انعامی!»
43 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka ce wa mutanen Yahuda, “Muna da rabo goma a wurin sarki; ban da haka ma, muna da hakki mafi yawa a wurin Dawuda fiye da ku. Don me kuke mana reni? Ba mu ne ma muka fara magana dawowa da sarki ba?” Amma mutanen Yahuda suka ɗauka maganar da zafi fiye da mutanen Isra’ila.
مردان اسرائیل جواب دادند: «ولی اسرائیل ده قبیله است. پس اکثریت با ماست و ما ده برابر بیشتر از شما به گردن پادشاه حق داریم. چرا با نظر حقارت به ما نگاه می‌کنید؟ فراموش نکنید که موضوع بازگرداندن پادشاه را ما پیشنهاد کردیم.» این بحث و گفتگو ادامه یافت، اما سخنان مردان یهودا از سخنان مردان اسرائیل قویتر بود.

< 2 Sama’ila 19 >