< 2 Sama’ila 19 >
1 Aka faɗa wa Yowab cewa, “Sarki yana kuka, yana kuma makoki saboda Absalom.”
I javiše Joabu: “Eno kralj plače i tuguje za Abšalomom.”
2 Saboda haka sai nasarar da aka yi a ranar ta zama makoki ga dukan sojoji, gama a ranar, rundunoni sun ji an ce, “Sarki yana baƙin ciki domin ɗansa.”
Tako se pobjeda u onaj dan pretvorila u žalost za svu vojsku, jer je vojska čula u onaj dan da kralj tuguje za svojim sinom.
3 Mutane fa suka shiga birni shiru, sai ka ce waɗanda sukan sace jiki don kunya sa’ad da suka gudo daga yaƙi.
I toga se dana vojskom kradom vrati u grad, kao što se kradom šulja vojska koja se osramotila bježeći iz boja.
4 Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da ƙarfi yana cewa, “Ya ɗana Absalom! Ya Absalom ɗana, ɗana!”
A kralj je pokrio svoje lice i vapio iza glasa: “Sine moj Abšalome! Abšalome, sine moj! Sine moj!”
5 Sai Yowab ya shiga gidan sarki ya ce, “Yau ka kunyatar da dukan mutanenka, waɗanda ba da daɗewa ba sun ceci ranka, da rayukan’ya’yanka maza, da na’ya’yanka mata, da na matanka da kuma na ƙwarƙwaranka.
Tada Joab dođe kralju u kuću i reče mu: “Postiđuješ danas lice svih svojih slugu koji su danas spasili život tebi, život tvojim sinovima i tvojim kćerima, život tvojim ženama i život inočama tvojim,
6 Kana ƙaunar maƙiyinka, kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Ka bayyana a fili cewa komandodi da sojojinsu ba kome ba ne a gare ka. Na ga cewa da za ka yi farin ciki, da a ce Absalom yana da rai a yau, dukanmu kuma mun mutu.
jer iskazuješ ljubav onima koji te mrze, a mržnju onima koji te ljube. Danas si pokazao da ti ništa nije ni do vojvoda ni do vojnika, jer vidim sada da bi ti sasvim pravo bilo kad bi Abšalom bio živ, a mi svi da smo danas poginuli.
7 Yanzu ka fita ka ƙarfafa mutanenka. Na rantse da Ubangiji, in ba ka fita ba, babu mutum guda da za a bari tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni fiye da kowace irin masifar da ta auko maka tun ƙuruciyarka har zuwa yanzu.”
Zato sada ustani, iziđi i prijazno progovori svojim vojnicima; jer, kunem ti se Jahvom, ako ne iziđeš, nijedan čovjek neće ostati noćas s tobom, i to će ti biti veća nesreća od svih koje su te snašle od tvoje mladosti pa do sada.”
8 Saboda haka sarki ya tashi, ya zauna a bakin hanyar shiga. Da aka faɗa wa mutane cewa, “Sarki yana zaune a bakin hanyar shiga,” sai duk suka zo gabansa. Ana cikin haka, Isra’ilawa dai sun riga sun tsere zuwa gidajensu.
Kralj ustade i sjede na vrata. Javiše to svemu narodu govoreći: “Eno kralj sjedi na vratima.” I sav narod dođe pred kralja. A Izraelci bijahu pobjegli svaki u svoj šator.
9 Mutane ko’ina a kabilan Isra’ila, suka yi ta gardama da juna, suna cewa, “Sarki ne ya cece mu daga hannun abokan gābanmu, shi ne kuma ya kuɓutar da mu daga hannun Filistiyawa. Amma ga shi ya tsere daga ƙasar saboda Absalom;
I sav se narod po svim Izraelovim plemenima prepirao govoreći: “Kralj nas je izbavio iz ruku naših neprijatelja, on nas je izbavio iz ruku filistejskih, a sada je morao pobjeći iz zemlje ispred Abšaloma.
10 kuma shi Absalom, da muka naɗa yă yi mulkinmu, ya mutu a yaƙi. Saboda haka don me ba kwa ce wani abu game da dawo da sarki?”
A Abšalom koga smo pomazali za kralja poginuo je u boju. Zašto se, dakle, kolebate dovesti kralja natrag?”
11 Sai Sarki Dawuda ya aika da saƙo zuwa wurin Zadok da Abiyatar, firistoci, ya ce, “Ku tambayi dattawan Yahuda, ‘Me ya sa ku ne za ku zama na ƙarshe a yin tunanin komar da sarki zuwa fada, da yake abin da ake faɗi ko’ina a Isra’ila ya kai kunnen sarki a mazauninsa?
Te riječi svega Izraela dopru do kralja u njegovu kuću. Zato kralj David poruči svećenicima Sadoku i Ebjataru: “Recite starješinama judejskim ovako: 'Zašto da vi budete posljednji koji će kralja dovesti u njegovu kuću?
12 Ku’yan’uwana ne, jikina, jinina kuma. To, don me za ku zama na ƙarshe na yarda a dawo da sarki zuwa fada?’
Vi ste moja braća, vi ste od moga mesa i od mojih kosti. Zašto biste, dakle, bili posljednji koji će dovesti kralja natrag?'
13 Ku kuma ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba jikina ba ne da jinina? Allah yă hukunta ni, da hukunci mai tsanani, idan daga yanzu ba ka zama komandan sojojina a maimakon Yowab ba.’”
Recite i Amasi: 'Nisi li ti od mojih kosti i od moga mesa? Neka mi Bog učini zlo i neka mi doda drugo ako mi ne budeš zauvijek vojvoda nad mojom vojskom namjesto Joaba!'”
14 Ta haka ya rinjayi zukatan dukan mutane Yahuda, kamar mutum ɗaya. Suka aika da saƙo wurin sarki suka ce, “Ka dawo, kai da dukan mutanenka.”
Tada se složiše svi ljudi Judina roda kao jedan čovjek i poručiše kralju: “Vrati se sa svim svojim ljudima!”
15 Sa’an nan sarki ya dawo, ya kuma tafi har zuwa Urdun. To, mutanen Yahuda suka zo Gilgal don su fita su taryi sarki, su kuma kawo shi ƙetaren Urdun.
I tako se kralj vrati i dođe do Jordana, a Judejci bijahu stigli do Gilgala dolazeći u susret kralju da prate kralja na prijelazu preko Jordana.
16 Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuda don su taryi Sarki Dawuda.
Tada je pohitio i Šimej, sin Gerin, Benjaminovac iz Bahurima, i sišao s Judejcima u susret kralju Davidu.
17 Tare da shi akwai kabilar Benyamin mutum dubu, tare da Ziba, mai hidimar gidan Shawulu, da’ya’yansa maza goma sha biyar, da bayi ashirin. Suka ruga zuwa Urdun, inda sarki yake.
Imao je sa sobom tisuću ljudi od Benjaminova plemena. I Siba, sluga Šaulova doma, sa petnaest svojih sinova i dvadeset svojih slugu, dođe do Jordana pred kralja.
18 Suka haye a mashigin don su ƙetaro da iyalin sarki, su kuma yi duk abin da yake so. Sa’ad da Shimeyi ɗan Gera ya haye Urdun, sai ya fāɗi rubda ciki a gaban sarki
Dovezli su splav da prevezu kraljevu čeljad i da učine sve što bi mu bilo drago. A Gerin sin Šimej baci se pred noge kralju kad je kralj htio prijeći preko Jordana;
19 ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka riƙe laifina a zuciya. Kada ka tuna da laifin da na yi maka ranka yă daɗe, ranan nan da kake gudu daga Urushalima. Kada ka tuna da shi ko kaɗan.
i reče kralju: “Neka mi moj gospodar ne upiše u grijeh! Ne opominji se zla što ti ga je učinio tvoj sluga u onaj dan kad je moj gospodar i kralj izlazio iz Jeruzalema. Neka to kralj ne uzima k srcu!
20 Na sani ni bawanka na yi maka laifi. Shi ya sa na zama na farko daga dukan Gidan Yusuf, da mutanen Isra’ila wanda ya fito don yă tarye ka yau, ranka yă daɗe, sarki.”
Tvoj sluga uviđa da je sagriješio; zato sam, evo, došao danas prvi iz svega Josipova doma da siđem u susret svome gospodaru i kralju.”
21 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce, “Bai kamata a kashe Shimeyi saboda wannan ba? Ya la’anci shafaffe na Ubangiji.”
Ali Sarvijin sin Abišaj progovori i reče: “Zar Šimej ne zaslužuje smrt što je proklinjao pomazanika Jahvina?”
22 Dawuda ya ce, “Me ya haɗa ni da ku, ku’ya’yan Zeruhiya? Yau ɗin nan kun zama maƙiyana! Ya kamata a kashe wani a Isra’ila a yau? Ban san cewa yau ni sarki ne a bisa Isra’ila ba?”
A David odgovori: “Što ja imam s vama, Sarvijini sinovi, te me danas uvodite u napast? Zar bi danas mogao tko biti pogubljen u Izraelu? TÓa sada znam da sam danas opet kralj nad Izraelom.”
23 Saboda haka sarki ya ce wa Shimeyi, “Ba za ka mutu ba.” Sarki kuwa ya yi alkawari har da rantsuwa.
Tada kralj reče Šimeju: “Nećeš poginuti!” I kralj mu se zakle.
24 Mefiboshet, jikan Shawulu, shi ma ya gangara don yă taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har ran da ya komo lafiya, Mefiboshet bai lura da ƙafafunsa, ko yă aske gemunsa, ko yă wanke tufafinsa ba.
I Šaulov sin Meribaal sišao je u susret kralju. On nije njegovao ni svojih nogu ni svojih ruku, nije uređivao svoje brade, nije prao svojih haljina od onoga dana kad je otišao kralj pa sve do dana kad se opet vratio u miru.
25 Sa’ad da ya zo daga Urushalima don yă taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba Mefiboshet?”
Kad je iz Jeruzalema došao u susret kralju, upita ga kralj: “Zašto nisi pošao sa mnom, Meribaale?”
26 Sai ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, da yake bawanka gurgu ne, na ce, ‘A sa mini sirdi a kan jakina don in hau in tafi tare da sarki.’ Amma Ziba bawana ya bashe ni.
A on odgovori: “Kralju gospodaru! Moj me sluga prevario. Tvoj mu je sluga rekao: 'Osamari mi magaricu da je uzjašem i pođem s kraljem!' Jer tvoj je sluga hrom.
27 Ya kuwa ɓata suna bawanka a gaban ranka yă daɗe, sarki. Ranka yă daɗe, sarki yana kama da mala’ikan Allah, ka yi abin da ka ga ya fi maka kyau.
On je oklevetao tvoga slugu pred mojim gospodarom i kraljem. Ali moj je gospodar i kralj kao Božji anđeo: zato čini što je dobro u tvojim očima.
28 Duk zuriyar kakana ba su cancanci kome ba sai mutuwa daga ranka yă daɗe, amma ka ba wa bawanka wuri cikin mutanen da suke ci a teburinka. Saboda haka, wanda’yanci nake da shi da zan yi wani ƙarin roƙo a wurin sarki?”
Jer sav moj očinski dom nije bio drugo zaslužio nego smrt od moga gospodara kralja, a ti si ipak primio svoga slugu među one koji jedu za tvojim stolom. Pa kako još imam pravo tužiti se kralju?”
29 Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”
A kralj mu odgovori: “Čemu da još duljiš svoj govor? Određujem: ti i Siba podijelite njive!”
30 Mefiboshet ya ce wa sarki, “Bari yă ɗauki kome, yanzu da ranka yă daɗe, sarki ya dawo gida lafiya.”
Meribaal reče kralju: “Neka uzme i sve, kad se moj gospodar kralj sretno vratio u svoj dom!”
31 Barzillai mutumin Gileyad shi ma ya zo daga Rogelim don yă ƙetare Urdun tare da sarki, yă kuma sallame shi daga can.
I Barzilaj Gileađanin dođe iz Rogelima i nastavi s kraljem da ga isprati preko Jordana.
32 To, Barzillai fa tsoho ne, mai shekara tamanin. Ya tanada wa sarki a lokaci da yake Mahanayim, gama shi attajiri ne.
Barzilaj bijaše vrlo star, bilo mu je osamdeset godina. Pribavljao je kralju opskrbu dok je boravio u Mahanajimu jer bijaše vrlo imućan čovjek.
33 Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka ƙetaro tare da ni ka zauna tare da ni a Urushalima, zan kuwa tanada maka.”
Kralj reče Barzilaju: “Pođi sa mnom, ja ću te u tvojim starim danima uzdržavati kod sebe u Jeruzalemu.”
34 Amma Barzillai ya ce wa sarki, “Shekara nawa ya rage mini har da zan tafi Urushalima da sarki?
A Barzilaj odgovori kralju: “A koliko mi još godina života ostaje da idem s kraljem u Jeruzalem?
35 Yanzu ina da shekara tamanin. Zan iya bambanta abu mai daɗi da marar daɗi kuma ne? Bawanka zai iya jin ɗanɗano abin da yake ci, ko yake sha ne? Har yanzu zan iya jin muryoyin mawaƙan maza da mata? Don me bawanka zai zama ƙari kaya ga ranka yă daɗe?
Sada mi je osamdeset godina; mogu li još razlikovati što je dobro a što zlo? Može li tvojem sluzi još goditi što jede i pije? Mogu li još slušati glas pjevača i pjevačica? Zašto bi tvoj sluga bio još na teret mome gospodaru kralju?
36 Bawanka zai ƙetare Urdun tare da sarki, yă ɗan yi maka rakiya kaɗan. Me ya sa ranka yă daɗe zai ba ni irin wannan lada.
Tvoj će sluga još samo prijeći preko Jordana s kraljem, ali zašto bi mi kralj dao takvu nagradu?
37 Ka bar bawanka yă koma, don in mutu a garina, kusa da kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ga bawanka Kimham. Bari yă ƙetare tare da ranka yă daɗe, sarki. Ka yi abin da ka ga dama da shi.”
Dopusti svome sluzi da se vrati, da umrem u svom gradu kod groba svoga oca i svoje majke. Ali evo tvoga sluge Kimhama, neka ide dalje s mojim gospodarom kraljem, pa njemu učini što je dobro u tvojim očima!”
38 Sarki ya ce, “Kimham zai ƙetare tare da ni, zan kuwa yi masa abin da ya gamshe ka. Kuma duk abin da kake bukata a wurina, zan yi maka.”
Kralj odgovori: “Neka onda Kimham ide sa mnom dalje, a ja ću mu učiniti što bude tebi drago i što god me zamoliš sve ću mu učiniti za tebe.”
39 Saboda haka dukan mutane suka ƙetare Urdun, sa’an nan kuma sarki ma ya ƙetare. Sarki ya yi wa Barzillai sumba ya albarkace shi, sa’an nan Barzillai ya koma gidansa.
Kad je sav narod prešao preko Jordana, prijeđe i kralj, poljubi Barzilaja i blagoslovi ga, potom se ovaj vrati u svoje mjesto.
40 Sa’ad da sarki ya ƙetare zuwa Gilgal, Kimham ma ya ƙetare tare da shi. Dukan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra’ila suka ƙetare da sarki.
Kralj nastavi put u Gilgal, a Kimham iđaše s njim. Kralja je pratio sav narod Judin i polovina naroda Izraelova.
41 Nan take sai ga mutane Isra’ila suna zuwa wurin sarki, suna cewa, “Don me’yan’uwanmu, mutanen Yahuda, suka saci sarki, suka kawo shi da iyalinsa a ƙetaren Urdun, tare da dukan mutanensa?”
Uto svi Izraelci dođu pred kralja i upitaju ga: “Zašto te naša braća Judejci ukradoše i zašto prevedoše preko Jordana našega kralja i njegov dom i sve Davidove ljude s njim?”
42 Dukan mutanen Yahuda suka ce wa mutanen Isra’ila, “Mun yi haka domin sarki danginmu na kurkusa ne. Don me kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abu daga cikin kayan sarki ne? Mun ɗauki wani abu wa kanmu ne?”
A Juda odgovori Izraelu: “Kralj je meni rod. Zašto si se ražestio zbog toga? Jesam li jeo na kraljev račun? Ili sam si što prigrabio?”
43 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka ce wa mutanen Yahuda, “Muna da rabo goma a wurin sarki; ban da haka ma, muna da hakki mafi yawa a wurin Dawuda fiye da ku. Don me kuke mana reni? Ba mu ne ma muka fara magana dawowa da sarki ba?” Amma mutanen Yahuda suka ɗauka maganar da zafi fiye da mutanen Isra’ila.
Tada Izrael odgovori Judi ovako: “Ja imam deset udjela na kralja i prema tebi ja sam prvorođenac. Zašto si me, dakle, prezreo? Nije li moja riječ bila prva kad je trebalo natrag dovesti moga kralja?” Ali govor Judin bijaše tvrđi od govora Izraelova.