< 2 Sama’ila 18 >
1 Dawuda ya tattara mutanen da suke tare da shi, ya naɗa musu komandodi na dubu-dubu, da na ɗari-ɗari.
David contou as pessoas que estavam com ele, e colocou capitães de milhares e capitães de centenas sobre eles.
2 Dawuda ya sa rundunoni kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Yowab, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Abishai, ɗan’uwan Yowab ɗan Zeruhiya, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Ittai mutumin Gat. Sai sarki ya ce wa rundunonin, “Tabbatacce zan tafi tare da ku.”
David enviou o povo, uma terceira parte sob a mão de Joab, e uma terceira parte sob a mão de Abishai, filho de Zeruiah, irmão de Joab, e uma terceira parte sob a mão de Ittai, o Gittita. O rei disse ao povo: “Eu também certamente sairei com você”.
3 Amma mutanen suka ce, “Ba za ka fita ba; gama in ya kasance tilas mu gudu, ba za su kula da mu ba. Ko da rabinmu sun mutu, ba za su damu ba; amma kai kanka ka fi mutum dubu goma namu. Zai fi maka ka zauna a cikin gari, ka dinga aika mana da taimako.”
Mas o povo disse: “Vocês não sairão, pois se fugirmos, eles não se importarão conosco, nem se metade de nós morrer, eles se importarão conosco. Mas vocês valem dez mil de nós. Portanto, agora é melhor que você esteja pronto para nos ajudar a sair da cidade”.
4 Sarki ya ce, “Zan yi duk abin da ya fi muku kyau.” Saboda haka sarki ya tsaya kusa da bakin ƙofa yayinda dukan mutane suke fitowa a ƙungiyar ɗari-ɗari da ta dubu-dubu.
O rei lhes disse: “Farei o que lhe parecer melhor”. O rei ficou ao lado do portão, e todo o povo saiu às centenas e aos milhares.
5 Sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai, ya ce musu, “Ku yi mini hankali da saurayin nan Absalom.” Dukan mutane kuwa suka ji yadda sarki yake ba wa kowane komanda umarni.
O rei comandou Joab e Abishai e Ittai, dizendo: “Lidem gentilmente, por mim, com o jovem Absalom”. Todo o povo ouviu quando o rei ordenou a todos os capitães a respeito de Absalom.
6 Rundunonin suka tafi zuwa fili don su yi yaƙi da Isra’ila. Aka kuwa yi yaƙi a kurmin Efraim.
Então o povo foi para o campo contra Israel; e a batalha foi na floresta de Efraim.
7 A nan ne mutanen Isra’ila suka sha kashi a hannun mutanen Dawuda. Waɗanda suka yi rauni da kuma waɗanda suka mutu a ranar sun yi yawa, mutum dubu ashirin.
O povo de Israel foi atingido lá diante dos servos de Davi, e houve uma grande matança naquele dia de vinte mil homens.
8 Yaƙin ya bazu a duk fāɗin ƙauyukan, abin da kurmin ya ci kawai a ranar ya fi yawan abin da aka kashe da takobi.
Pois a batalha estava ali espalhada pela superfície de todo o país, e a floresta devorou mais pessoas naquele dia do que a espada devorou.
9 To, Absalom ya haɗu da mutanen Dawuda. Yana hawan dokinsa, kuma yayinda dokin ya kusa kai cikin rassan babban itacen oak, sai kan Absalom ya sarƙafe a kan itacen oak ɗin. Dokin ya wuce da gudu, shi kuwa ya rataye a can yana lilo.
Absalom conheceu por acaso os criados de David. Absalom estava montado em sua mula, e a mula foi para debaixo dos ramos grossos de um grande carvalho; e sua cabeça pegou o carvalho, e ele estava pendurado entre o céu e a terra; e a mula que estava debaixo dele continuou.
10 Sa’ad da wani daga cikin mutanen ya gan haka, sai ya gaya wa Yowab, “Na ga Absalom yana rataye a itacen oak.”
Um certo homem o viu, disse a Joab, e disse: “Eis que eu vi Absalom pendurado num carvalho”.
11 Yowab ya ce wa mutumin da ya ba shi labarin, “Mene! Ka ga shi? Don me ba ka buge shi har ƙasa nan da nan ba? Ai, da na ba ka shekel goma na azurfa da abin ɗamarar jarumi.”
Joab disse ao homem que lhe disse: “Eis que você o viu, e por que você não o atingiu lá no chão? Eu lhe teria dado dez moedas de prata e uma faixa”.
12 Amma mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a auna mini azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba. A kunnuwanmu fa sarki ya umarce ka, da Abishai, da Ittai cewa, ‘Ku tsare saurayin nan Absalom a madadina.’
O homem disse a Joab: “Embora eu devesse receber mil moedas de prata em minha mão, eu ainda não estenderia minha mão contra o filho do rei; pois em nossa audiência o rei ordenou a você e Abishai e Ittai, dizendo: 'Cuidado para que ninguém toque no jovem Absalom'.
13 Da na yi haka da na sa kaina a halin ƙaƙa-ni-ka-yi, kuma babu abin da zai ɓoyu ga sarki, kai kuwa za ka janye abinka daga gare ni.”
Caso contrário, se eu tivesse agido falsamente contra sua vida (e não há matéria escondida do rei), então você mesmo teria se colocado contra mim”.
14 Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci da kai ba.” Saboda haka sai ya ɗauki māsu uku a hannunsa ya zura su a ƙahon zuciyar Absalom, tun Absalom yana da sauran rai a maƙale a itacen oak.
Então Joab disse: “Eu não vou esperar assim com você”. Ele pegou três dardos na mão e os empurrou através do coração de Absalom enquanto ainda estava vivo no meio do carvalho.
15 Masu ɗaukan kayan yaƙin Yowab goma kuwa sun kewaye Absalom, suka bubbuge shi suka kashe.
Dez jovens que carregaram a armadura de Joab cercaram e atingiram Absalom, e o mataram.
16 Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, sai sojoji suka bar fafaran Isra’ila, gama Yowab ya tsai da su.
Joab tocou a trombeta, e o povo voltou de perseguir Israel; pois Joab reteve o povo.
17 Suka ɗauki Absalom, suka jefa shi cikin wani babban rami a kurmin, suka kuwa tula tsibin duwatsu a kansa. Ana cikin haka, sai dukan Isra’ilawa suka tsere zuwa gidajensu.
Eles pegaram Absalom e o lançaram em um grande poço na floresta, e levantaram sobre ele um monte de pedras muito grande. Então todo Israel fugiu, cada um para sua própria tenda.
18 A lokacin da Absalom yake da rai, Absalom ya gina wa kansa al’amudin tunawa, a Kwarin Sarki, gama ya yi tunani ya ce, “Ba ni da ɗa namiji wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Sai ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kuwa kira shi Al’amudin Absalom har wa yau.
Agora Absalom em sua vida havia tomado e criado para si o pilar que está no vale do rei, pois ele disse: “Não tenho nenhum filho para manter meu nome na memória”. Ele chamou o pilar com o seu próprio nome. É chamado de monumento de Absalom, até os dias de hoje.
19 Ahimawaz ɗan Zadok ya ce, “Bari in ruga in kai wa sarki labari cewa Ubangiji ya cece shi daga hannun abokan gābansa.”
Então Ahimaaz, filho de Zadok, disse: “Deixe-me agora correr e levar a notícia do rei, como Javé o vingou de seus inimigos”.
20 Yowab ya ce, “Ba kai ba ne za ka kai wannan labari a yau ba. Kana iya kai labarin wani lokaci, amma yau kam ba zai yiwu ba, saboda ɗan sarki ya mutu.”
Joab disse-lhe: “Você não deve ser o portador de notícias hoje, mas deve levar notícias em outro dia”. Mas hoje você não deve levar notícias, porque o filho do rei está morto”.
21 Sai Yowab ya ce wa wani mutumin Kush, “Je ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Mutumin Kush ɗin kuwa ya rusuna wa Yowab, sai ya ruga a guje.
Então Joab disse ao Cushite: “Vá, diga ao rei o que você viu”! O Cushite se curvou diante de Joab, e correu.
22 Ahimawaz ɗan Zadok ya sāke ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru, ina roƙonka bari in bi bayan mutumin Kush nan.” Amma Yowab ya ce, “Ɗana me ya sa kake so ka je? Ba ka da labarin da zai jawo maka lada.”
Então Ahimaaz, o filho de Zadok, disse mais uma vez a Joab: “Mas, aconteça o que acontecer, por favor, deixe-me também correr atrás do Cushite”. Joab disse: “Por que você quer correr, meu filho, já que não terá nenhuma recompensa pela notícia?”
23 Ya ce, “Ko mene ne zai faru, ina so in ruga da gudu.” Sai Yowab ya ce, “Ruga!” Sai Ahimawaz ya sheƙa a guje ya bi ta hanyar fili ya riga mutumin Kush nan.
“Mas aconteça o que acontecer”, disse ele, “eu vou correr”. Ele disse a ele: “Corra!”. Então Ahimaaz correu pelo caminho da Planície, e ultrapassou o Cushite.
24 Yayinda Dawuda yake zaune tsakanin ƙofofin ciki da na waje, sai mai tsaro ya hau rufin ginin da yake kan hanyar shiga ta wajen katanga. Da ya duba sai ya ga wani mutum shi kaɗai yana gudu.
Agora David estava sentado entre os dois portões; e o vigia subiu até o teto do portão para o muro, levantou os olhos e olhou, e eis que um homem corria sozinho.
25 Mai tsaro ya tā da murya ya faɗa wa sarki. Sarki ya ce, “In shi kaɗai ne, ya kawo labari mai kyau ke nan.” Mutumin ya matso kusa-kusa.
O sentinela gritou e disse ao rei. O rei disse: “Se ele está sozinho, há novidades em sua boca”. Ele se aproximou cada vez mais.
26 Sai mai tsaron ya ga wani mutum yana zuwa a guje. Sai ya tā da murya ya kira mai tsaron ƙofa ya ce, “Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai!” Sarki ya ce, “Shi ma yana kawo labari mai daɗi ne.”
O vigilante viu outro homem correndo; e o vigilante chamou o porteiro e disse: “Eis um homem correndo sozinho”! O rei disse: “Ele também traz novidades”.
27 Sai mai tsaron ya ce, “A ganina gudu na farin, ya yi kama da gudun Ahimawaz, ɗan Zadok.” Sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana zuwa da saƙo mai kyau.”
O vigia disse: “Acho que a corrida do primeiro é como a corrida de Ahimaaz, o filho de Zadok”. O rei disse: “Ele é um bom homem, e vem com boas notícias”.
28 Sai Ahimawaz ya tā da murya ya ce wa sarki, “Kome lafiya yake!” Sai ya rusuna har ƙasa a gaban sarki ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka! Ya ba da mutanen da suka tayar wa ranka yă daɗe a hannunsa.”
Ahimaaz chamou, e disse ao rei: “Tudo está bem”. Ele se curvou diante do rei com o rosto na terra, e disse: “Bendito seja Javé, vosso Deus, que entregou os homens que levantaram a mão contra meu senhor, o rei”!
29 Sai sarki ya ce, “Saurayin nan Absalom yana nan da rai?” Ahimawaz ya ce, “Na ga wani babban rikicewar a daidai lokacin da Yowab yake gab da aikan bawan sarki da kuma ni, sai dai ban san ko mene ne ba.”
O rei disse: “Está tudo bem com o jovem Absalom”? Ahimaaz respondeu: “Quando Joab enviou o servo do rei, até mesmo eu seu servo, vi um grande tumulto, mas não sei o que era”.
30 Sai sarki ya ce, “Koma gefe ka jira a can.” Sai ya ja gefe ya tsaya.
O rei disse: “Venha e fique aqui”. Ele veio e ficou parado.
31 Sai ga mutumin Kush ya iso ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, ka ji labari mai kyau! Ubangiji ya cece ka yau daga dukan waɗanda suka tayar maka.”
Eis que veio o Cushite. O Cushite disse: “Boas notícias para meu senhor, o rei, pois Javé vingou-vos hoje de todos aqueles que se levantaram contra vós”.
32 Sarki ya ce wa mutumin Kush, “Saurayin nan Absalom, yana nan lafiya?” Mutumin Kush ya ce, “Allah yă sa abokan gāban ranka yă daɗe, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.”
O rei disse ao Cushite: “Está tudo bem com o jovem Absalom”? O Cushite respondeu: “Que os inimigos de meu senhor, o rei, e todos os que se levantam contra vós para fazer-vos mal, sejam como aquele jovem é”.
33 Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”
The o rei ficou muito emocionado, e subiu para a sala por cima do portão e chorou. Ao ir, ele disse: “Meu filho Absalom! Meu filho, meu filho Absalom! Quem me dera ter morrido ao invés de você, Absalom, meu filho, meu filho”!