< 2 Sama’ila 18 >

1 Dawuda ya tattara mutanen da suke tare da shi, ya naɗa musu komandodi na dubu-dubu, da na ɗari-ɗari.
David mønstret folket som var med ham, og satte høvedsmenn over dem, nogen over tusen og nogen over hundre.
2 Dawuda ya sa rundunoni kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Yowab, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Abishai, ɗan’uwan Yowab ɗan Zeruhiya, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Ittai mutumin Gat. Sai sarki ya ce wa rundunonin, “Tabbatacce zan tafi tare da ku.”
Så sendte David folket avsted, en tredjedel under Joab, en tredjedel under Abisai, Serujas sønn, Joabs bror, og en tredjedel under gittitten Ittai, og kongen sa til folket: Jeg vil og dra ut med eder.
3 Amma mutanen suka ce, “Ba za ka fita ba; gama in ya kasance tilas mu gudu, ba za su kula da mu ba. Ko da rabinmu sun mutu, ba za su damu ba; amma kai kanka ka fi mutum dubu goma namu. Zai fi maka ka zauna a cikin gari, ka dinga aika mana da taimako.”
Men folket sa: Du skal ikke dra ut; for om vi flykter, bryr ingen sig om oss, og om halvdelen av oss faller, bryr heller ingen sig om oss; men du er så god som ti tusen av oss, og nu er det bedre at du er rede til å komme oss til hjelp fra byen.
4 Sarki ya ce, “Zan yi duk abin da ya fi muku kyau.” Saboda haka sarki ya tsaya kusa da bakin ƙofa yayinda dukan mutane suke fitowa a ƙungiyar ɗari-ɗari da ta dubu-dubu.
Da sa kongen til dem: Jeg skal gjøre som I synes. Så stilte kongen sig ved siden av porten, og alt folket drog ut, hundrevis og tusenvis.
5 Sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai, ya ce musu, “Ku yi mini hankali da saurayin nan Absalom.” Dukan mutane kuwa suka ji yadda sarki yake ba wa kowane komanda umarni.
Og kongen bød Joab og Abisai og Ittai og sa: Far varsomt med den unge mann - med Absalom! Og alt folket hørte på at kongen gav alle høvedsmennene dette påbud om Absalom.
6 Rundunonin suka tafi zuwa fili don su yi yaƙi da Isra’ila. Aka kuwa yi yaƙi a kurmin Efraim.
Så drog folket ut i marken mot Israel, og det kom til slag i Efra'imskogen.
7 A nan ne mutanen Isra’ila suka sha kashi a hannun mutanen Dawuda. Waɗanda suka yi rauni da kuma waɗanda suka mutu a ranar sun yi yawa, mutum dubu ashirin.
Der blev Israels folk slått av Davids menn, og det blev et stort mannefall der den dag - tyve tusen mann.
8 Yaƙin ya bazu a duk fāɗin ƙauyukan, abin da kurmin ya ci kawai a ranar ya fi yawan abin da aka kashe da takobi.
Og striden bredte sig ut over hele landet deromkring, og skogen fortærte den dag flere av folket enn sverdet fortærte.
9 To, Absalom ya haɗu da mutanen Dawuda. Yana hawan dokinsa, kuma yayinda dokin ya kusa kai cikin rassan babban itacen oak, sai kan Absalom ya sarƙafe a kan itacen oak ɗin. Dokin ya wuce da gudu, shi kuwa ya rataye a can yana lilo.
Absalom kom like imot Davids menn; han red på sitt muldyr, og muldyret kom inn under de tette grener på en stor terebinte, så hans hode hang fast i terebinten, og han blev hengende mellem himmel og jord; for muldyret som han satt på, løp sin vei.
10 Sa’ad da wani daga cikin mutanen ya gan haka, sai ya gaya wa Yowab, “Na ga Absalom yana rataye a itacen oak.”
Dette fikk en mann se, meldte det til Joab og sa: Jeg så Absalom henge i terebinten der borte.
11 Yowab ya ce wa mutumin da ya ba shi labarin, “Mene! Ka ga shi? Don me ba ka buge shi har ƙasa nan da nan ba? Ai, da na ba ka shekel goma na azurfa da abin ɗamarar jarumi.”
Da sa Joab til mannen som meldte ham dette: Men når du har sett det, hvorfor slo du ham da ikke til jorden med det samme? Så hadde det vært min skyldighet å gi dig ti sekel sølv og et belte.
12 Amma mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a auna mini azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba. A kunnuwanmu fa sarki ya umarce ka, da Abishai, da Ittai cewa, ‘Ku tsare saurayin nan Absalom a madadina.’
Men mannen sa til Joab: Om jeg så fikk mig tilveid tusen sekel sølv midt op i hånden, vilde jeg ikke rekke ut min hånd mot kongens sønn; for vi hørte alle på at kongen bød dig og Abisai og Ittai og sa: Vær varsom med den unge mann, med Absalom, hvem det så er av eder!
13 Da na yi haka da na sa kaina a halin ƙaƙa-ni-ka-yi, kuma babu abin da zai ɓoyu ga sarki, kai kuwa za ka janye abinka daga gare ni.”
Men om jeg hadde gått svikefullt frem og tatt hans liv, så blir jo ingen ting skjult for kongen, og du vilde nok holde dig unda.
14 Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci da kai ba.” Saboda haka sai ya ɗauki māsu uku a hannunsa ya zura su a ƙahon zuciyar Absalom, tun Absalom yana da sauran rai a maƙale a itacen oak.
Da sa Joab: Jeg kan ikke stå her med dig og hefte mig bort. Og han tok tre kastespyd i sin hånd og støtte dem i Absaloms hjerte, mens han ennu hang levende midt i terebinten.
15 Masu ɗaukan kayan yaƙin Yowab goma kuwa sun kewaye Absalom, suka bubbuge shi suka kashe.
Så stilte ti unge menn - Joabs våbensvenner - sig rundt omkring og hugg til Absalom og drepte ham.
16 Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, sai sojoji suka bar fafaran Isra’ila, gama Yowab ya tsai da su.
Da støtte Joab i basunen, og folket holdt op med å forfølge Israel; for Joab holdt folket tilbake.
17 Suka ɗauki Absalom, suka jefa shi cikin wani babban rami a kurmin, suka kuwa tula tsibin duwatsu a kansa. Ana cikin haka, sai dukan Isra’ilawa suka tsere zuwa gidajensu.
Og de tok Absalom og kastet ham i en stor grøft i skogen og reiste en stor stenrøs over ham; og hele Israel flyktet, hver til sitt hjem.
18 A lokacin da Absalom yake da rai, Absalom ya gina wa kansa al’amudin tunawa, a Kwarin Sarki, gama ya yi tunani ya ce, “Ba ni da ɗa namiji wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Sai ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kuwa kira shi Al’amudin Absalom har wa yau.
Men Absalom hadde, mens han levde, tatt og reist sig den støtte som står i Kongedalen; for han sa: Jeg har ingen sønn som kan holde oppe minnet om mitt navn. Han gav støtten navn efter sig selv, og den er blitt kalt Absaloms minnesmerke inntil denne dag.
19 Ahimawaz ɗan Zadok ya ce, “Bari in ruga in kai wa sarki labari cewa Ubangiji ya cece shi daga hannun abokan gābansa.”
Akima'as, Sadoks sønn, sa til Joab: La mig få springe avsted til kongen med det gledelige budskap at Herren har hjulpet ham til hans rett mot hans fiender!
20 Yowab ya ce, “Ba kai ba ne za ka kai wannan labari a yau ba. Kana iya kai labarin wani lokaci, amma yau kam ba zai yiwu ba, saboda ɗan sarki ya mutu.”
Men Joab sa til ham: Ikke vil du idag bli en mann med gledelig budskap; en annen dag kan du komme med gledelig budskap; men idag vilde du ikke komme med noget gledelig budskap, siden kongens sønn er død.
21 Sai Yowab ya ce wa wani mutumin Kush, “Je ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Mutumin Kush ɗin kuwa ya rusuna wa Yowab, sai ya ruga a guje.
Derefter sa Joab til kusitten: Gå og meld kongen hvad du har sett! Og kusitten bøide sig for Joab og sprang avsted.
22 Ahimawaz ɗan Zadok ya sāke ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru, ina roƙonka bari in bi bayan mutumin Kush nan.” Amma Yowab ya ce, “Ɗana me ya sa kake so ka je? Ba ka da labarin da zai jawo maka lada.”
Men Akima'as, Sadoks sønn, tok atter til orde og sa til Joab: Det får gå som det vil, men la også mig få springe avsted efter kusitten! Joab sa: Hvorfor vil du endelig gjøre det, min sønn? Du har jo ikke noget gledelig budskap som du kunde få lønn for.
23 Ya ce, “Ko mene ne zai faru, ina so in ruga da gudu.” Sai Yowab ya ce, “Ruga!” Sai Ahimawaz ya sheƙa a guje ya bi ta hanyar fili ya riga mutumin Kush nan.
Han svarte: Det får gå som det vil, jeg springer avsted. Og han sa til ham: Så spring da! Da sprang Akima'as bort efter veien gjennem Jordansletten og kom forbi kusitten.
24 Yayinda Dawuda yake zaune tsakanin ƙofofin ciki da na waje, sai mai tsaro ya hau rufin ginin da yake kan hanyar shiga ta wajen katanga. Da ya duba sai ya ga wani mutum shi kaɗai yana gudu.
Imidlertid satt David mellem begge portene, og vekteren gikk på taket over porten, bort på muren, og så utover. Da fikk han se en mann som kom springende alene.
25 Mai tsaro ya tā da murya ya faɗa wa sarki. Sarki ya ce, “In shi kaɗai ne, ya kawo labari mai kyau ke nan.” Mutumin ya matso kusa-kusa.
Vekteren ropte og meldte det til kongen. Da sa kongen: Er han alene, så er det et gledelig budskap i hans munn. Og han kom nærmere og nærmere.
26 Sai mai tsaron ya ga wani mutum yana zuwa a guje. Sai ya tā da murya ya kira mai tsaron ƙofa ya ce, “Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai!” Sarki ya ce, “Shi ma yana kawo labari mai daɗi ne.”
Da så vekteren en annen mann som kom springende, og vekteren ropte til portneren og sa: Se, det kommer en mann springende alene. Da sa kongen: Han kommer og med gledelig budskap.
27 Sai mai tsaron ya ce, “A ganina gudu na farin, ya yi kama da gudun Ahimawaz, ɗan Zadok.” Sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana zuwa da saƙo mai kyau.”
Og vekteren sa: Jeg synes den første springer så likt Akima'as, Sadoks sønn. Kongen sa: Det er en god mann; han kommer med godt budskap.
28 Sai Ahimawaz ya tā da murya ya ce wa sarki, “Kome lafiya yake!” Sai ya rusuna har ƙasa a gaban sarki ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka! Ya ba da mutanen da suka tayar wa ranka yă daɗe a hannunsa.”
Og Akima'as ropte til kongen: Fred! Og han kastet sig på sitt ansikt til jorden for kongen og sa: Lovet være Herren din Gud, som har gitt de menn som løftet sin hånd mot min herre kongen, i din makt!
29 Sai sarki ya ce, “Saurayin nan Absalom yana nan da rai?” Ahimawaz ya ce, “Na ga wani babban rikicewar a daidai lokacin da Yowab yake gab da aikan bawan sarki da kuma ni, sai dai ban san ko mene ne ba.”
Og kongen sa: Står det vel til med den unge mann - med Absalom? Akima'as svarte: Jeg så det var et stort opstyr, da Joab sendte kongens tjener og mig, din tjener, avsted; men jeg vet ikke hvad det var.
30 Sai sarki ya ce, “Koma gefe ka jira a can.” Sai ya ja gefe ya tsaya.
Kongen sa: Gå til side og stå der! Så gikk han til side og blev stående der.
31 Sai ga mutumin Kush ya iso ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, ka ji labari mai kyau! Ubangiji ya cece ka yau daga dukan waɗanda suka tayar maka.”
Straks efter kom kusitten, og han sa: Min herre kongen motta det gledelige budskap at Herren idag har hjulpet dig til din rett mot alle dem som hadde reist sig imot dig!
32 Sarki ya ce wa mutumin Kush, “Saurayin nan Absalom, yana nan lafiya?” Mutumin Kush ya ce, “Allah yă sa abokan gāban ranka yă daɗe, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.”
Kongen spurte kusitten: Står det vel til med den unge mann - med Absalom? Kusitten svarte: Gid det må gå min herre kongens fiender og alle som reiser sig imot dig og vil gjøre ondt, som det gikk den unge mann!
33 Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”
Da blev kongen dypt rystet. Han gikk op på salen over porten og gråt, og mens han gikk, sa han så: Min sønn Absalom! Min sønn, min sønn Absalom! O, at jeg var død i ditt sted! Absalom, min sønn, min sønn!

< 2 Sama’ila 18 >