< 2 Sama’ila 18 >

1 Dawuda ya tattara mutanen da suke tare da shi, ya naɗa musu komandodi na dubu-dubu, da na ɗari-ɗari.
HELU aku la o Davida i na kanaka me ia, a hoonoho aku la i na lunatausani, a me na lunahaneri maluna o lakou.
2 Dawuda ya sa rundunoni kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Yowab, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Abishai, ɗan’uwan Yowab ɗan Zeruhiya, kashi ɗaya bisa uku a ƙarƙashin Ittai mutumin Gat. Sai sarki ya ce wa rundunonin, “Tabbatacce zan tafi tare da ku.”
Hoouna aku la o Davida i ka hapakolu o na kanaka malalo o ka lima o Ioaba, a o kekahi hapakolu malalo o ka lima o Abisai ke keiki a Zeruia, o ko Ioaba kaikaina, a o kekahi hapakolu malalo o ka lima o Itai ke Giti. I aku la hoi ke alii i na kanaka, Owau io no kekahi e hele aku ana me oukou.
3 Amma mutanen suka ce, “Ba za ka fita ba; gama in ya kasance tilas mu gudu, ba za su kula da mu ba. Ko da rabinmu sun mutu, ba za su damu ba; amma kai kanka ka fi mutum dubu goma namu. Zai fi maka ka zauna a cikin gari, ka dinga aika mana da taimako.”
Aka, i mai la na kanaka, Aole oe e hele aku; no ka mea, a i hee aku makou, aole lakou e manao mai ia makou; a i make hoi kekahi hapalua o makou, aole no hoi lakou e manao mai ia makou. Aka hoi, ua like oe me ka umi tausani o makou; nolaila, e aho nau e kokua mai ia makou mailoko mai o ke kulanakauhale.
4 Sarki ya ce, “Zan yi duk abin da ya fi muku kyau.” Saboda haka sarki ya tsaya kusa da bakin ƙofa yayinda dukan mutane suke fitowa a ƙungiyar ɗari-ɗari da ta dubu-dubu.
I aku la ke alii ia lakou, O ka oukou pono ka'u e hana'i. Ku ae la ke alii ma ka aoao o ka ipuka o ka pa, a haele mai la na kanaka a pau iwaho ma na haneri a ma na tausani.
5 Sarki ya umarci Yowab, Abishai, da Ittai, ya ce musu, “Ku yi mini hankali da saurayin nan Absalom.” Dukan mutane kuwa suka ji yadda sarki yake ba wa kowane komanda umarni.
Kauoha aku la ke alii ia Ioaba me Abisai a me Itai, i aku la, E ahonui aku oukou no'u i ke kanaka opiopio ia Abesaloma. A lohe ae la na kanaka a pau, i ka wa i kauoha aku ai ke alii i na lunakoa a pau no Abesaloma.
6 Rundunonin suka tafi zuwa fili don su yi yaƙi da Isra’ila. Aka kuwa yi yaƙi a kurmin Efraim.
Alaila hele aku la na kanaka iwaho ma ke kula e ku e i ka Iseraela: aia ma ka ululaau o Eperaima ke kaua ana.
7 A nan ne mutanen Isra’ila suka sha kashi a hannun mutanen Dawuda. Waɗanda suka yi rauni da kuma waɗanda suka mutu a ranar sun yi yawa, mutum dubu ashirin.
Ilaila ua pepehiia na kanaka o ka Iseraela imua o ka poe kauwa a Davida: a he luku nui no ia la ma ia wahi, o na kanaka he iwakalua tausani.
8 Yaƙin ya bazu a duk fāɗin ƙauyukan, abin da kurmin ya ci kawai a ranar ya fi yawan abin da aka kashe da takobi.
No ka mea, kaua liilii lakou malaila maluna o ka aina a pau: a ua oi ka nui o ka poe i make i ka laau ia la, i ka poe i make i ka pahikaua.
9 To, Absalom ya haɗu da mutanen Dawuda. Yana hawan dokinsa, kuma yayinda dokin ya kusa kai cikin rassan babban itacen oak, sai kan Absalom ya sarƙafe a kan itacen oak ɗin. Dokin ya wuce da gudu, shi kuwa ya rataye a can yana lilo.
A halawai ae la o Abesaloma me na kauwa a Davida. A holo ae la o Abesaloma maluna o ka hoki, a hele aku la ka hoki malalo o na lala pilikia o kekahi laau oka nui, a hihia ae la kona poo i ka laau, a kaulia oia mawaena o ka lani a o ka honua, a hele aku la ka hoki mai lalo aku ona.
10 Sa’ad da wani daga cikin mutanen ya gan haka, sai ya gaya wa Yowab, “Na ga Absalom yana rataye a itacen oak.”
Ike aku la kekahi kanaka ia mea, a hai aku la ia Ioaba, i aku la, Aia ua ike aku au ia Abesaloma e kau ana maloko o kekahi laau oka.
11 Yowab ya ce wa mutumin da ya ba shi labarin, “Mene! Ka ga shi? Don me ba ka buge shi har ƙasa nan da nan ba? Ai, da na ba ka shekel goma na azurfa da abin ɗamarar jarumi.”
I mai la o Ioaba i ke kanaka nana i hai aku ia ia, Aia hoi, ua ike aku oe; heaha hoi kau i pepehi ole ai ia ia a haule ia i ka houna? alaila haawi aku no wau ia oe i na apana kala he umi a me kekahi kaei.
12 Amma mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a auna mini azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba. A kunnuwanmu fa sarki ya umarce ka, da Abishai, da Ittai cewa, ‘Ku tsare saurayin nan Absalom a madadina.’
I aku la ua kanaka la ia Ioaba, Ina paha e kau ana ma kun lima na apana kala he tausani, aole au e o aku i kuu lima e pepehi i ke keiki a ke alii: no ka mea, i ko makou lohe ana, ua kauoha mai ke alii ia oe, me Abisai a me Itai, i mai la, E malama oukou a pau i ke kanaka opiopio ia Abesaloma.
13 Da na yi haka da na sa kaina a halin ƙaƙa-ni-ka-yi, kuma babu abin da zai ɓoyu ga sarki, kai kuwa za ka janye abinka daga gare ni.”
Ina ole pela, ina ua hana au ma ka wahahee e hihia ai ko'u ola: no ka mea, aohe mea i hunaia mai ke alii aku, a o oe no hoi kekahi e ku e ia'u.
14 Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci da kai ba.” Saboda haka sai ya ɗauki māsu uku a hannunsa ya zura su a ƙahon zuciyar Absalom, tun Absalom yana da sauran rai a maƙale a itacen oak.
Alaila, i aku la o Ioaba, Aole au e pono ke kali wale penei imua ou. Lalau aku la ia i na ihe ekolu ma kona lima, a hou aku la ia mau mea maloko o ka puu o Abesaloma, oi ola kela mawaena o ka laau oka.
15 Masu ɗaukan kayan yaƙin Yowab goma kuwa sun kewaye Absalom, suka bubbuge shi suka kashe.
Hoopuni mai la ka poe umi nana i lawe i ka Ioaba mea kaua, pepehi aku la ia Abesaloma, a make iho la ia.
16 Sa’an nan Yowab ya busa ƙaho, sai sojoji suka bar fafaran Isra’ila, gama Yowab ya tsai da su.
Puhi aku la o Ioaba i ka pu, a hoi mai la na kanaka mai ke alualu ana'ku i ka Iseraela: no ka mea, ua paa na kanaka ia Ioaba.
17 Suka ɗauki Absalom, suka jefa shi cikin wani babban rami a kurmin, suka kuwa tula tsibin duwatsu a kansa. Ana cikin haka, sai dukan Isra’ilawa suka tsere zuwa gidajensu.
Lawe aku la lakou ia Abesaloma; a hoolei aku la ia ia maloko o ka lua nui ma ka ululaau, a kau aku la lakou i ahu pohaku nui maluna iho ona: a holo aku la ka Iseraela a pau, o kela mea keia mea i kona halelewa.
18 A lokacin da Absalom yake da rai, Absalom ya gina wa kansa al’amudin tunawa, a Kwarin Sarki, gama ya yi tunani ya ce, “Ba ni da ɗa namiji wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Sai ya kira ginshiƙin da sunansa, ana kuwa kira shi Al’amudin Absalom har wa yau.
A o Abesaloma i kona wa e ola ana, lawe aku la ia a hooku ae la i kekahi kia pohaku ma ke awawa o ke alii: no ka mea, i aku la ia, Aole a'u keikikane nana e hoomau i kuu inoa; a kapa aku la ia i ua kia pohaku la ma kona inoa iho: a ua kapaia'ku ia ko Abesaloma wahi, a hiki i neia manawa.
19 Ahimawaz ɗan Zadok ya ce, “Bari in ruga in kai wa sarki labari cewa Ubangiji ya cece shi daga hannun abokan gābansa.”
Alaila i aku la o Ahimaaza ke keiki a Zadoka, E ae mai oe e holo aku au ano, e lawe aku i ka olelo i ke alii, ua hoopakele aku o Iehova ia ia mai na lima aku o kona poe enemi.
20 Yowab ya ce, “Ba kai ba ne za ka kai wannan labari a yau ba. Kana iya kai labarin wani lokaci, amma yau kam ba zai yiwu ba, saboda ɗan sarki ya mutu.”
I mai la o Ioaba ia ia, Aole no oe e lawe aku i ka olelo i keia la; e lawe olelo oe i kekahi la ae: i keia la, aole oe e lawe olelo aku, no ka mea, ua make ke keikikane a ke alii.
21 Sai Yowab ya ce wa wani mutumin Kush, “Je ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Mutumin Kush ɗin kuwa ya rusuna wa Yowab, sai ya ruga a guje.
Alaila i aku la o Ioaba ia Kusi, O hele oe e hai i ke alii i ka mea au i ike iho nei. Kulou iho la o Kusi ia Ioaba, a holo aku la.
22 Ahimawaz ɗan Zadok ya sāke ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru, ina roƙonka bari in bi bayan mutumin Kush nan.” Amma Yowab ya ce, “Ɗana me ya sa kake so ka je? Ba ka da labarin da zai jawo maka lada.”
I hou aku la o Ahimaaza ke keiki a Zadoka ia Ioaba, Owau hoi kekahi, ke noi aku nei au ia oe, e holo aku au mahope o Kusi. I mai la o Ioaba, No ke aha hoi oe e holo aku ai, e kuu keiki, aohe olelo e pono nau?
23 Ya ce, “Ko mene ne zai faru, ina so in ruga da gudu.” Sai Yowab ya ce, “Ruga!” Sai Ahimawaz ya sheƙa a guje ya bi ta hanyar fili ya riga mutumin Kush nan.
E ae mai hoi oe e holo wau. I mai la kela ia ia, E holo. Alaila holo aku la o Ahimaaza ma ka aoao o ka papu, a oi aku la ia imua o Kusi.
24 Yayinda Dawuda yake zaune tsakanin ƙofofin ciki da na waje, sai mai tsaro ya hau rufin ginin da yake kan hanyar shiga ta wajen katanga. Da ya duba sai ya ga wani mutum shi kaɗai yana gudu.
Noho iho la o Davida mawaena o na puka elua o ka pa, a pii aku la ke kiai maluna o ka puka ma ka pa pohaku; alawa ae la kona mau maka, nana aku la, aia he kanaka e holo mai ana, oia wale no.
25 Mai tsaro ya tā da murya ya faɗa wa sarki. Sarki ya ce, “In shi kaɗai ne, ya kawo labari mai kyau ke nan.” Mutumin ya matso kusa-kusa.
Hea mai la ke kiai, a hai mai la i ke alii. I aku la ke alii, Ina hookahi wale no oia, he olelo no ma kona waha. Neenee mai la no ia, a kokoke mai.
26 Sai mai tsaron ya ga wani mutum yana zuwa a guje. Sai ya tā da murya ya kira mai tsaron ƙofa ya ce, “Duba, ga wani mutum kuma yana gudu shi kaɗai!” Sarki ya ce, “Shi ma yana kawo labari mai daɗi ne.”
Ike aku la hoi ke kiai i kekahi kanaka e ae e holo mai ana: hea mai la ke kiai i ka malama puka, Aia hoi, he kanaka e holo hookahi mai ana. I aku la ke alii, Ke lawe mai nei hoi oia i ka olelo.
27 Sai mai tsaron ya ce, “A ganina gudu na farin, ya yi kama da gudun Ahimawaz, ɗan Zadok.” Sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana zuwa da saƙo mai kyau.”
I mai la ke kiai, Ua like ka mea holo mua i kuu manao me ka holo ana o Ahimaaza ke keiki a Zadoka. I aku la ke alii, He kanaka maikai ia, a ke hele mai nei ia me ka olelo maikai.
28 Sai Ahimawaz ya tā da murya ya ce wa sarki, “Kome lafiya yake!” Sai ya rusuna har ƙasa a gaban sarki ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka! Ya ba da mutanen da suka tayar wa ranka yă daɗe a hannunsa.”
Kahea mai la o Ahimaaza, i mai la i ke alii, Aloha oe. A haule iho la ia ilalo ke alo ma ka honua imua o ke alii, i mai la, E hoomaikaiia o Iehova o kou Akua, nana i hoolilo mai i ka poe kanaka i hookiekie ae i ko lakou lima e ku e i kuu haku i ke alii.
29 Sai sarki ya ce, “Saurayin nan Absalom yana nan da rai?” Ahimawaz ya ce, “Na ga wani babban rikicewar a daidai lokacin da Yowab yake gab da aikan bawan sarki da kuma ni, sai dai ban san ko mene ne ba.”
I aku la ke alii, Ua malama ola ia ke kanaka opio, o Abesaloma? I mai la o Ahimaaza, A hoouna mai la o Ioaba i ke kauwa a ke alii, a ia'u hoi i kau kauwa, ua ike aku au i ka wawa nui, aole hoi au i ike i ke ano.
30 Sai sarki ya ce, “Koma gefe ka jira a can.” Sai ya ja gefe ya tsaya.
I aku la ke alii, E kipa ae oe a e ku maanei. Kipa ae la ia, a ku malie iho la.
31 Sai ga mutumin Kush ya iso ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, ka ji labari mai kyau! Ubangiji ya cece ka yau daga dukan waɗanda suka tayar maka.”
Aia hoi, hele mai la o Kusi: i mai la o Kusi, He olelo ka'u e kuu haku, e ke alii; ua hoapono mai o Iehova ia oe i keia la i ka poe a pau i hoea mai e ku e ia oe.
32 Sarki ya ce wa mutumin Kush, “Saurayin nan Absalom, yana nan lafiya?” Mutumin Kush ya ce, “Allah yă sa abokan gāban ranka yă daɗe, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.”
I aku la ke alii ia Kusi, Ua malama ola ia anei ke kanaka opio o Abesaloma? I mai la o Kusi, O ka poe enemi o kuu haku o ke alii, a o ka poe a pau i ku e mai e hoino mai ia oe, e hoolikeia lakou me ua kanaka opio la.
33 Sai gaban sarki ya faɗi. Ya haura zuwa ɗakin da yake kan katangar hanyar shiga ya yi kuka. Yayinda yake tafiya ya ce, “Ya ɗana Absalom! Ɗana, ɗana Absalom! Da ma a ce ni ne na mutu maimakonka. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”
Haaloulou nui iho la ke alii, a pii aku la i ke keena maluna o ka puka, a uwe iho la: a i kona hele ana, penei kana i olelo ai, Auwe! kuu keiki e Abesaloma e! e kuu keiki, kuu keiki e Abesaloma e! ina no wau i make nou, e Abesaloma kuu keiki, kuu keiki e!

< 2 Sama’ila 18 >