< 2 Sama’ila 17 >
1 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
Ahitofel Avşalom'a şöyle dedi: “İzin ver de on iki bin kişi seçeyim, bu gece kalkıp Davut'un peşine düşeyim.
2 Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
Davut yorgun ve güçsüzken ona saldırıp gözünü korkutayım. Yanındakilerin hepsi kaçacaktır. Ben de yalnız Kral Davut'u öldürürüm.
3 in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
Sonra bütün halkı sana geri getiririm. Halkın dönmesi, öldürmek istediğin adamın ölümüne bağlıdır. Böylece halk da esenlikte olur.”
4 Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
Bu öğüt Avşalom'u ve İsrail ileri gelenlerini hoşnut etti.
5 Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
Avşalom, “Arklı Huşay'ı da çağırın, neler söyleyeceğini duyalım” dedi.
6 Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
Huşay gelince Avşalom, “Ahitofel bu öğüdü verdi” dedi, “Onun öğüdüne uyalım mı? Yoksa, sen öğüt ver.”
7 Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
Huşay Avşalom'a, “Bu kez Ahitofel'in verdiği öğüt iyi değil” dedi,
8 Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
“Baban Davut'la adamlarının güçlü savaşçılar olduklarını biliyorsun. Kırda yavrularından yoksun bırakılmış bir ayı gibi öfkeliler. Baban deneyimli bir savaşçıdır, geceyi askerlerle geçirmez.
9 Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
Şu anda ya bir mağarada ya da başka bir yerde gizlenmiştir. Davut askerlerine karşı ilk saldırıyı yapınca, bunu her duyan, ‘Avşalom'u destekleyenler arasında kırım var’ diyecek.
10 Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
O zaman aslan yürekli yiğitler bile korkuya kapılacak. Çünkü bütün İsrailliler babanın güçlü, yanındakilerin de yiğit olduğunu bilir.
11 “Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
“Onun için sana öğüdüm şu: Dan'dan Beer-Şeva'ya kadar, kıyıların kumu kadar olan İsrailliler çevrene toplansın, sen de savaşa katıl.
12 Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
O zaman gizlendiği yerlerden birinde Davut'un üstüne yürürüz; yeryüzüne düşen çiy gibi üzerine gideriz. Onu da, yanındakilerin hiçbirini de yaşatmayız.
13 In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
Eğer bir kente çekilirse, İsrailliler o kente halatlar getirir, tek bir taş kalmayıncaya dek kenti vadiye indiririz.”
14 Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
Avşalom'la İsrailliler, “Arklı Huşay'ın öğüdü Ahitofel'in öğüdünden daha iyi” dediler. Çünkü RAB, Avşalom'u yıkıma uğratmak için, Ahitofel'in iyi öğüdünü boşa çıkarmayı tasarlamıştı.
15 Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
Huşay Kâhin Sadok'la Kâhin Aviyatar'a şöyle dedi: “Ahitofel Avşalom'a ve İsrail'in ileri gelenlerine böyle öğüt verdi, bense şöyle öğüt verdim.
16 Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
Şimdi siz Davut'a hemen şu haberi gönderin: ‘Geceyi kırdaki ırmağın sığ yerinde geçirme, duraksamadan karşı yakaya geç; yoksa kral da yanındakilerin tümü de yok olabilir.’”
17 Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
Bu sırada Yonatan'la Ahimaas Eyn-Rogel'de kalıyorlardı. Bir hizmetçi kız gidip onlara olup bitenleri haber veriyor, onlar da gidip duyduklarını Kral Davut'a bildiriyorlardı. Çünkü kendileri kente girerken görünmeyi göze alamıyorlardı.
18 Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
Ama bir genç onları görüp Avşalom'a bildirdi. Bunun üzerine Yonatan'la Ahimaas hemen oradan ayrılıp Bahurim'de bir adamın evine gittiler. Evin avlusunda bir kuyu vardı. Yonatan'la Ahimaas kuyuya indiler.
19 Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
Adamın karısı bir örtü alıp kuyunun ağzına serdi. Bir şey belli olmasın diye örtünün üstüne başak yaydı.
20 Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
Avşalom'un görevlileri eve, kadının yanına varınca, “Ahimaas'la Yonatan nerede?” diye sordular. Kadın, “Irmağın karşı yakasına geçtiler” diye yanıtladı. Avşalom'un görevlileri onları aramaya gittiler; bulamayınca Yeruşalim'e döndüler.
21 Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
Adamlar gittikten sonra, Ahimaas'la Yonatan kuyudan çıktılar ve olup bitenleri bildirmek üzere Kral Davut'a gittiler. Ona, “Haydi, hemen ırmağı geçin” dediler, “Çünkü Ahitofel size karşı böyle öğüt verdi.”
22 Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
Bunun üzerine Davut'la yanındaki bütün halk Şeria Irmağı'nı çabucak geçti. Şafak söktüğünde Şeria Irmağı'nı geçmeyen bir kişi bile kalmamıştı.
23 Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
Ahitofel, verdiği öğüde uyulmadığını görünce, eşeğine palan vurdu; yola koyulup kentine, evine döndü. İşlerini düzene koyduktan sonra kendini astı. Ölüsünü babasının mezarına gömdüler.
24 Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
Davut Mahanayim'e vardığı sırada Avşalom'la yanındaki İsrail askerleri Şeria Irmağı'nı geçtiler.
25 Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
Avşalom Yoav'ın yerine Amasa'yı ordu komutanı atamıştı. Amasa Yitra adında bir İsmaili'nin oğluydu. Annesi Nahaş'ın kızı Avigayil'di; Yoav'ın annesi Seruya'nın kızkardeşiydi.
26 Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
Avşalom'la İsrailliler Gilat bölgesinde ordugah kurdular.
27 Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
Davut Mahanayim'e vardığında, Ammonlular'ın Rabba Kenti'nden Nahaş oğlu Şovi, Lo-Devarlı Ammiel oğlu Makir ve Rogelim'den Gilatlı Barzillay ona yataklar, taslar, toprak kaplar getirdiler. Ayrıca Davut'la yanındakilerin yemesi için buğday, arpa, un, kavrulmuş buğday, bakla, mercimek, bal, tereyağı, inek peyniri ve koyun da getirdiler. “Halk kırda yorulmuştur, aç ve susuzdur” diye düşünmüşlerdi.
28 suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”